Home General Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 da ya gabata na jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya ce matakin dakatar da ministar jin ƙai da yaƙi da talauci, Betta Edu, abin yabawa ne,ko da yake bai isa ba.

Shugaba Tinubu ya dakatar da ministar ne a jiya Litinin kuma ya umarci hukumar EFCC ta gudanar da bincike a kanta, bayan ya fuskanci kiraye-kirayen a ɗauki mataki a kanta saboda zarge-zargen tafka almundahana, ko da yake ta musanta zarge-zargen.

Ministar da aka dakatar ta dai fuskanci gagarumar suka ne bayan kwarmata wasu takardun kashe kuɗi daga ma’aikatarta, waɗanda suka nuna ta bayar da umarni ga babbar akanta ta biya naira miliyan 585 cikin wani asusun ajiyar wata, lamarin da ake zargin ya saɓa ƙa’idojin kashe kuɗi na gwamnati.

A cikin wata wasiƙa da wani mataimakinsa na musamman Phrank Shaibu ya fitar, jagoran adawar Najeriya ya ce abin takaici ne ganin yadda shirin da aka kafa don tsamo ‘yan Najeriya miliyan 100 daga matsanancin talauci amma kamar yadda ake zargi ya zama saniyar tatsa ga gwamnatocin jam’iyyar APC.

Ya ce, “Ko da yake Tinubu ya cancanci yabo saboda dakatar da Betta Edu, amma mun yi imani, yunƙurin ya zo a makare. Da farko, ba shi da wata alaƙa ta naɗa ta a matsayin minista ta irin wannan muhimmiyar ma’aikata. Sai dai Tinubu ya fifita siyasa a kan ƙwarewa, lamarin da ya janyo wannan abin kunya.

Atiku wanda ya yi kira a yi wa ma’aikatar garambawul, ya kuma yi zargin cewa ba Betta Edu kaɗai ba ce da hannu a wannan badaƙala.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp