Home General Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Atiku ya yabawa Tinubu kan yaki da cin hanci da Rashawa

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 da ya gabata na jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya ce matakin dakatar da ministar jin ƙai da yaƙi da talauci, Betta Edu, abin yabawa ne,ko da yake bai isa ba.

Shugaba Tinubu ya dakatar da ministar ne a jiya Litinin kuma ya umarci hukumar EFCC ta gudanar da bincike a kanta, bayan ya fuskanci kiraye-kirayen a ɗauki mataki a kanta saboda zarge-zargen tafka almundahana, ko da yake ta musanta zarge-zargen.

Ministar da aka dakatar ta dai fuskanci gagarumar suka ne bayan kwarmata wasu takardun kashe kuɗi daga ma’aikatarta, waɗanda suka nuna ta bayar da umarni ga babbar akanta ta biya naira miliyan 585 cikin wani asusun ajiyar wata, lamarin da ake zargin ya saɓa ƙa’idojin kashe kuɗi na gwamnati.

A cikin wata wasiƙa da wani mataimakinsa na musamman Phrank Shaibu ya fitar, jagoran adawar Najeriya ya ce abin takaici ne ganin yadda shirin da aka kafa don tsamo ‘yan Najeriya miliyan 100 daga matsanancin talauci amma kamar yadda ake zargi ya zama saniyar tatsa ga gwamnatocin jam’iyyar APC.

Ya ce, “Ko da yake Tinubu ya cancanci yabo saboda dakatar da Betta Edu, amma mun yi imani, yunƙurin ya zo a makare. Da farko, ba shi da wata alaƙa ta naɗa ta a matsayin minista ta irin wannan muhimmiyar ma’aikata. Sai dai Tinubu ya fifita siyasa a kan ƙwarewa, lamarin da ya janyo wannan abin kunya.

Atiku wanda ya yi kira a yi wa ma’aikatar garambawul, ya kuma yi zargin cewa ba Betta Edu kaɗai ba ce da hannu a wannan badaƙala.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp