Home General ‘Yan Bindiga sun hallaka mutane 10 a jihar Katsina

‘Yan Bindiga sun hallaka mutane 10 a jihar Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

Ƴan bindiga sun afkawa kauyen Kukar Babangida da ke karamar hukumar Jibia ta jihar Katsina, inda suka hallaka dagacin kauyen Magaji Haruna da ɗansa.

manema labarai a kasar sun ruwaito cewa an kuma kashe wasu mutum takwas a harin da aka kai da misalin karfe 10 na dare ranar Laraba.

Har ila yau, wani mazaunin garin ya bayyana cewa an tafi da mata wanda ba a san adadinsu ba zuwa yanzu.

Mazauna garin sun yi imanin cewa akwai manyan shugabannin ƴan bindiga biyu da ke cin karensu babu babbaka a ciki da wajen karamar hukumar ta Jibia.

Ƙauyen Kukar Babangida ya kasance ɗaya daga cikin kauyuka da ke fama da matsalar ƴan bindiga tun bayyanar ayyukansu a faɗin jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp