Home Labarai Tinubu- za mu kawo karshen matsalar tattalin arziki a Nijeriya

Tinubu- za mu kawo karshen matsalar tattalin arziki a Nijeriya

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa ƴan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta shawo kan matsalar taɓarɓarewar tattalin arziki da kasar ke fama da shi, ciki har da sauko da hauhawar farashin kayayyaki.

Ya ce duk da cewa shi ba na daban bane, amma kada ‘yan Najeriya su damu saboda yana da zimmar kawo karshen hauhawar farashi.

Tinubu ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin kwamitin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC a wajen buɗe-baki a fadarsa da ke Abuja ranar Laraba, inda ya ce gwamnatinsa na aiki tukuru don sauko da farashin kayayyaki.

“Wannan alkawari ne mai wahala da kuka yi wa al’ummar Najeriya lokacin da kuke min yakin neman zaɓe, dole ne na yi aiki don tabbatar da haka.

“Na yi kamfe kan fata mai kyau, dole ne na ɗabbaka wannan fata da kuma fatan ganin kowaye cikinmu ya ji daɗi. Tattalin arzikinmu na kan turba mai kyau. Kada ku damu kan haka,” in ji Tinubu.

Ya ce Najeriya na fama da matsalar hauhawar farashi kuma a shirye gwamnatinsa take wajen magance ta.

“Muna sake fasalin harkokin kuɗir shigarmu, kuma muna samun nasara kan haka, kuma muna dawo da tagomashinmu a faɗin duniya,” in ji shugaban Najeriyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp