Home Labarai Almundahana – Abba Gida Gida zai binciki Ganduje

Almundahana – Abba Gida Gida zai binciki Ganduje

Gwamnatin jihar Kano ta kafa kwamatocin bincike biyu domin duba batun wadaƙa da kuɗin al’umma da rikicin siyasa da ɓatan mutane tsakanin 2015 da 2023 a tsukin zamanin mulkin mutumin da ya gada, Abdullahi Ganduje.

Yayin ƙaddamar da kwamatocin ranar Alhamis, gwamna Yusuf ya buƙaci mambobin da su yi aiki domin hukunta wanda yake da hannu.

Gwamnan ya ce gudanar da bincike kan almubazzaranci da kuɗaɗen al’umma wani ɓangare ne na alƙawarin da ya ɗauka a lokacin da ya sha rantsuwar kama aiki na bankaɗowa tare da gurfanar da mutanen da ke da hannu a rikice-rikicen siyasa da suka faru a jihar.

Ya bayyana yadda tashin hankali sakamakon rikicin siyasa ke janyo koma-baya ga dimokraɗiyya a faɗin duniya da kuma janyo asarar rayuka da rashin yarda a ɓangaren mutane da kuma waɗanda ke jagoranci.

Gwamnan ya ce bai kamata a ƙyale munanan rikice-rikicen siyasar da aka gani musamman a 2023 su wuce ba don a hana afkuwar haka a gaba.

Kwamitin farko, ƙarƙashin Zuwaira Yusuf zai duba rikicin siyasa da mutanen da suka ɓata daga 2015 zuwa 2023.

“Muna fatan a zaƙulo mutanen da ke da hannu tare da bayyana waɗanda suka tallafa domin su fuskanci hukunci a kuma gano dalilai da tashin hankalin da aka yi a 2015 da 2019 da 2013”. in ji gwamnan.

Kwamiti na biyu, bisa jagorancin Mai shari’a Faruk Lawan, ya samu umarnin gwamna Yusuf da ya duba ƙararrakin da suka shafi almubazzaranci da dukiyar al’umma da kadarorin gwamnati.

Gwamnan ya buƙaci mai shari’a Lawan da mambobin kwamitin da kada su yi ƙasa a gwiwa wajen gano almubazzarancin da aka yi musamman a ƙarƙashin gwamnatin da ta gabata.

A zaɓen da ya gabata ne aka kama, ɗan majalisar wakilai Alhassan Doguwa saboda zargin hannu a kisan da aka yi wa wasu da kuma tayar da rikici, Sai dai daga bisani an ba da belinsa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp