Home Labarai Ganduje – Zai fi dacewa Gwamnatin Abba ta fara bincike tun daga...

Ganduje – Zai fi dacewa Gwamnatin Abba ta fara bincike tun daga 1999

Shugaban jam’iyyar APC mai mulki a Nigeria, Abdullahi Umar Ganduje, ya zargi gwamna Abba Yusuf na jihar Kano da yin amfani da wasu dabaru wajen fakewa da boye gazawarsa da rashin tabuka komai ga al’umma tun da ya shiga Ofis.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Edwin Olofu, ya fitar ranar juma’a.

Ganduje yayi Martani ne kan wasu kwamitoci da gwamnatin jihar kano ta kafa domin bincikar yadda Ganduje ya yi tusarrafi da kudaden al’umma da kuma yadda aka yi ta fadan Siyasa a zamanin mulkinsa wanda har yayi asarar rayukan al’umma.

“A gaskiya babu wani abun azo a gani a jihar kano da gwamnan yayi da kudaden da gwamnatin tarayya karkashin Bola Ahmed Tinubu take turowa jihar kano”.

Ganduje ya kuma mayar da martani ne kan matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka na gurfanar da shi a gaban kotu bisa zarginsa da karbar cin hancin dala 413,000, da kuma Naira biliyan 1.38.

“Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta dage dole sai sun shafa min kashin kaji ni da Iyalaina, sai dai sun ƙasa ganewa cewa komai ana yin sa ne akan doron doka da oda” inji shi

“Sun kasa daukar matakin shari’a kan umarni da babbar kotun tarayya da ke Kano ta bayar kwanan nan, inda ta ce laifin da ake zargina da shi, laifi ne da gwamnatin tarayya ce take da hurumi, wanda babban lauyan gwamnatin tarayya da kuma hukumar EFCC ne kadai zasu iya gurfanar da ni akan shi”.

“Har yanzu suna da damar komawa kan tsarina na ci gaba mai dorewa wanda zai ciyar da jihar Kano gaba. Har yanzu bai makara ba don su yi koyi da ci gaban da na samar.”

Ganduje wanda ya mulki jihar a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023, ya kuma bayyana matakin da gwamnatin ta dauka na kafa kwamitoci biyu da za su gudanar da bincike a kansa kan zargin almubazzaranci da dukiyar al’umma da tashe-tashen hankula na siyasa da kuma bacewar mutanen a jihar a matsayin abin farin ciki.

Yace zai fi dacewa da cigaban jihar gwamnatin ta tsawaita wa’adin gudanar da binciken daga 1999 zuwa yau.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp