Home General Cikin watan Afrilu kadai an yi garkuwa da mutane sama da dari...

Cikin watan Afrilu kadai an yi garkuwa da mutane sama da dari uku a Nijeriya

Wani rahoton tsaro na kamfanin Beacon Consulting ya bayyana cewa yawan mutanen da aka hallaka a Najeriya cikin watan Afrilun 2024 ya zarce na watan Maris da ya gabata da kimanin kaso 34.4 cikin ɗari.

Rahoton tsaron na wata-wata wanda da kamfanin ke fitarwa ya nuna cewa a cikin watan na Afrilu an kashe mutum 1,097 yayin da a watan Maris aka kashe mutum 816.

Hakan a cewar rahoton “abu ne mai ban tsaro”, tare da bukatar hukumomi su ɗauki matakan da suka dace wajen daƙile matsalolin tsaron da ke haifar da irin waɗannan kashe-kashe.

Jihar da aka fi kashe mutane a cikin watan na Afrilu ita ce Borno, inda aka kashe mutum 367, sai Zamfara mai biye mata a matsayi na biyu, inda aka kashe mutum 113, yayin da Kano ta zo a matsayi na uku, inda aka kashe mutum 64.

Borno ce jihar da ta fi shan wahala sanadiyyar matsalar hare-haren ƴan ƙungiyar Boko Haram.

Duk da cewa gwamnatin Najeriya ta yi ƙoƙari wajen rage ayyukan mayaƙan na Boko Haram amma har yanzu akan samu hare-hare nan da can.

Haka nan mayaƙan na Boko Haram kan dasa nakiyoyi a hanyoyin ababen hawa, wani abu da ke haifar da asarar rayuka.

A ɓangaren garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa kuwa jihar Zamfara ce a gaba, inda aka yi garkuwa da mutum 122, sai Borno a matsayi na biyu, inda aka yi garkuwa da mutum 40, yayin da jihar Delta take a matsayi na uku, inda aka sace mutum 29.

Zamfara na daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar ƴan bindiga masu garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

Ƴan bindigan na kai hare-hare a ƙauyuka, inda suke satar dukiya da mutane domin neman kuɗin fansa.

Duk da cewa gwamnati na cewa tana bakin ƙoƙarinta wajen magance matsalar amma har yanzu matsalar na ci gaba da haifar da asarar rayuka da tagayyara al’umma a faɗin jihohin arewa maso yammacin ƙasar.

Rahoton ya bayyana cewa an yi garkuwa da mutum 311 yayin da aka raunata mutum 342 a cikin watan na Afrilu a faɗin Najeriya.

Sai dai a ɓangare guda rahoton ya ce an samu raguwar yawan kai hare-hare da kuma sace-sacen al’umma domin neman kuɗin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp