Home DUNIYA Ƴan sanda sun cafke matashin da ake zargi da cinna wa masallaci...

Ƴan sanda sun cafke matashin da ake zargi da cinna wa masallaci wuta a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta cafke wani matashi da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta a lokacin da mutane fiye da 30 ke sallar Asuba a ciki. lamarin dai ya faru ne a a ƙauyen Larabar Abasawa a ƙaramar hukumar Gezawa.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwar da rundunar ta fitar, mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce matashin mai suna Shafi’u Abubakar mai shekara 38 ya yi sanadiyyar ƙonewar mutane.

Tuni dai aka kwashe mutum 24 waɗanda suka ƙone zuwa asibiti domin a duba lafiyarsu.

SP Kiyawa ya ƙara da cewa binciken da aka gudanar dai ya nuna cewa an yi amfani da man fetir ne wajen cinna wutar.

Dangane kuma da dalilin faruwar al’amarin, SP Kiyawa ya ce “matashin ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon ƙin raba gado a tsakanin danganinsa, inda ya ce waɗanda suka zalunce shi ɗin suna cikin masallacin a lokacin da suke sallah. Kuma ya yi hakan ne domin ya aike da saƙo.” In ji matashin.

PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp