Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar shahararren dan ta’addan nan wanda ya addabi arewacin Nijeriya Buharin Yadi.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro da Al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan.

Wani barin wuta da dakarun sojojin Nijeriya na rundunar Operation Whirl Punch sukayi kan  maboyar dan ta’addan Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da (Alias Buharin Yadi) ta yi sanadiyyar mutuwar sa da wasu cikin mayakan sa a maboyar su.

Dakarun sojojin dake karkashin kwamandan sojoji dake lura da iyakar kananan hukumomin Giwa da Sabuwa dake Jihohin kaduna da Katsina Manjo Janar MLD Saraso, sun sami nasarar ne a daidai Idasu bisa wasu bayanan sirri da suka samu kan mayakan dake sintiri a yankunan Samunaka, saulawa dake jihar Katsina.

Bawan wani batakashi daya gudana tsakanin dakarun da mayakan bayan bankado maboyar su da dakarun sukayi abinda ya haddasa mutuwar shanu masu tarin yawa.

Kachalla buhari Alhaji Haladu wanda aka fi sani da Buharin Yadi ko kuma Buhari Janar da saran tawagar sun uzzirawa yankunan Kidandan/Galadimawa dake karamar hukumar, Sabon Birni/Kerawa dake karamar hukumar Igabi, Sabuwa dake jihohin Katsina Niger da Zamfara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp