Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar shahararren dan ta’addan nan wanda ya addabi arewacin Nijeriya Buharin Yadi.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro da Al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan.

Wani barin wuta da dakarun sojojin Nijeriya na rundunar Operation Whirl Punch sukayi kan  maboyar dan ta’addan Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da (Alias Buharin Yadi) ta yi sanadiyyar mutuwar sa da wasu cikin mayakan sa a maboyar su.

Dakarun sojojin dake karkashin kwamandan sojoji dake lura da iyakar kananan hukumomin Giwa da Sabuwa dake Jihohin kaduna da Katsina Manjo Janar MLD Saraso, sun sami nasarar ne a daidai Idasu bisa wasu bayanan sirri da suka samu kan mayakan dake sintiri a yankunan Samunaka, saulawa dake jihar Katsina.

Bawan wani batakashi daya gudana tsakanin dakarun da mayakan bayan bankado maboyar su da dakarun sukayi abinda ya haddasa mutuwar shanu masu tarin yawa.

Kachalla buhari Alhaji Haladu wanda aka fi sani da Buharin Yadi ko kuma Buhari Janar da saran tawagar sun uzzirawa yankunan Kidandan/Galadimawa dake karamar hukumar, Sabon Birni/Kerawa dake karamar hukumar Igabi, Sabuwa dake jihohin Katsina Niger da Zamfara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp