Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar shahararren dan ta’addan nan wanda ya addabi arewacin Nijeriya Buharin Yadi.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro da Al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan.

Wani barin wuta da dakarun sojojin Nijeriya na rundunar Operation Whirl Punch sukayi kan  maboyar dan ta’addan Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da (Alias Buharin Yadi) ta yi sanadiyyar mutuwar sa da wasu cikin mayakan sa a maboyar su.

Dakarun sojojin dake karkashin kwamandan sojoji dake lura da iyakar kananan hukumomin Giwa da Sabuwa dake Jihohin kaduna da Katsina Manjo Janar MLD Saraso, sun sami nasarar ne a daidai Idasu bisa wasu bayanan sirri da suka samu kan mayakan dake sintiri a yankunan Samunaka, saulawa dake jihar Katsina.

Bawan wani batakashi daya gudana tsakanin dakarun da mayakan bayan bankado maboyar su da dakarun sukayi abinda ya haddasa mutuwar shanu masu tarin yawa.

Kachalla buhari Alhaji Haladu wanda aka fi sani da Buharin Yadi ko kuma Buhari Janar da saran tawagar sun uzzirawa yankunan Kidandan/Galadimawa dake karamar hukumar, Sabon Birni/Kerawa dake karamar hukumar Igabi, Sabuwa dake jihohin Katsina Niger da Zamfara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp