Home General Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Babbar Kotun tarayya dake Jihar Kano a Arewacin Najeriya, ta ce tana da hurumin sauraron ƙarar da Alhaji Aminu Babba Ɗan agundi ya shigar akan batun dambarwar Masarautar Kano.
Kotun ƙarƙashin Jagorancin mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman tayi ƙwarya-ƙwaryar Hukuncin ne, biyo bayan inkarin da ɓangaren waɗanda ake ƙara suka yi na cewar kotun bata da hurumin sauraron ƙarar.
A zaman baya dai an tafka muhawara a tsakanin ɓangarorin biyu wato ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara akan batun hurumin kotun dangane da Shari’ar, harma kotun ta ayyana yau Alhamis a matsayin ranar da zata bayyana matsayar ta akan batun hurumin.
Kuma tuni kotun ta ɗage zaman Shari’ar zuwa ranar 26 ga watan nan na Yuni domin ci-gaba da sauraron shariar bayan ta tabbatar cewa tana da hurumin sauraron ƙarar.
Ɓangaren Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ne dai suka shigar da ƙarar, a sakamakon rashin amince wa da matakin Gwamnatin Kano na rushe Masarautun jihar guda biyar bayan da Majalisar dokokin jihar tayi wa dokar Masarautun Garambawul.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp