Home General Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Kotu nada hurumin saurarar karar Dambarwar Masarautar Kano – Kotu

Babbar Kotun tarayya dake Jihar Kano a Arewacin Najeriya, ta ce tana da hurumin sauraron ƙarar da Alhaji Aminu Babba Ɗan agundi ya shigar akan batun dambarwar Masarautar Kano.
Kotun ƙarƙashin Jagorancin mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman tayi ƙwarya-ƙwaryar Hukuncin ne, biyo bayan inkarin da ɓangaren waɗanda ake ƙara suka yi na cewar kotun bata da hurumin sauraron ƙarar.
A zaman baya dai an tafka muhawara a tsakanin ɓangarorin biyu wato ɓangaren masu ƙara da waɗanda ake ƙara akan batun hurumin kotun dangane da Shari’ar, harma kotun ta ayyana yau Alhamis a matsayin ranar da zata bayyana matsayar ta akan batun hurumin.
Kuma tuni kotun ta ɗage zaman Shari’ar zuwa ranar 26 ga watan nan na Yuni domin ci-gaba da sauraron shariar bayan ta tabbatar cewa tana da hurumin sauraron ƙarar.
Ɓangaren Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ne dai suka shigar da ƙarar, a sakamakon rashin amince wa da matakin Gwamnatin Kano na rushe Masarautun jihar guda biyar bayan da Majalisar dokokin jihar tayi wa dokar Masarautun Garambawul.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp