Home General Ma’aikatan PSC sun bukaci Tinubu ya Cire IG Egbetokun

Ma’aikatan PSC sun bukaci Tinubu ya Cire IG Egbetokun

Gamayyar kungiyoyin Ma’aikatan hukumar dake lura da ayyukan ‘yan sanda ta Nijeriya PSC ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu daya sauke shugaban rundunar ‘yan sandan kasar Kayode Egbetokun bisa yunkurin yin kafar ungulu a shirin daukar jami’an hukumar.

Yayin da take ganawa da manema labarai a birnin Abuja ranar laraba kungiyar ta zargi wasu cikin manyan jami’an hukumar da yunkurin cusa sunayen wadanda basu cancanta ba a lokacin jarabawar daukar aikin.

Mambobin kungiyar dake rera wakokin zanga – zanga, sun bayyana yunkurin rundunar ‘yan sandan na  na dauke hankula.

Kungiyar tace  NPF na kokarin kare shugaban kasa kada ya fahimci rashin shirin makarantun horar da ‘yan sanda da yadda suke a mawuyacin hali.

Wannan dai na zuwa ne bayan da hukumar dake lura da ayyukan ‘yan sanda ta saki sunayen mutum dubu 10 wadanda suka sami nasarar haye jarabawar daukar aikin dan sanda a Nijeriya.

Sai dai daga bisani hukumar ‘yan sandan ta yi fatali da jerin sunayen wanda tace akwai ayyukan damfara a cikin sa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp