Home General Ma’aikatan PSC sun bukaci Tinubu ya Cire IG Egbetokun

Ma’aikatan PSC sun bukaci Tinubu ya Cire IG Egbetokun

Gamayyar kungiyoyin Ma’aikatan hukumar dake lura da ayyukan ‘yan sanda ta Nijeriya PSC ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu daya sauke shugaban rundunar ‘yan sandan kasar Kayode Egbetokun bisa yunkurin yin kafar ungulu a shirin daukar jami’an hukumar.

Yayin da take ganawa da manema labarai a birnin Abuja ranar laraba kungiyar ta zargi wasu cikin manyan jami’an hukumar da yunkurin cusa sunayen wadanda basu cancanta ba a lokacin jarabawar daukar aikin.

Mambobin kungiyar dake rera wakokin zanga – zanga, sun bayyana yunkurin rundunar ‘yan sandan na  na dauke hankula.

Kungiyar tace  NPF na kokarin kare shugaban kasa kada ya fahimci rashin shirin makarantun horar da ‘yan sanda da yadda suke a mawuyacin hali.

Wannan dai na zuwa ne bayan da hukumar dake lura da ayyukan ‘yan sanda ta saki sunayen mutum dubu 10 wadanda suka sami nasarar haye jarabawar daukar aikin dan sanda a Nijeriya.

Sai dai daga bisani hukumar ‘yan sandan ta yi fatali da jerin sunayen wanda tace akwai ayyukan damfara a cikin sa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp