Home DUNIYA Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarunta sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda 125, tare da kama 200, inda suka sami nasarar kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su a wasu mabambanta hare hare da suka gudanar a kasar cikin mako daya.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada Labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba ya fitar a ranar juma’a yayin da yake bayar da bayani kan ayyukan rundunar a birnin Abuja.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito Buba na cewa dakarun sun kwato makamai 120, gami da alburusai 1,793, sai kuma bindiga kirar AK47 guda 56, da kuma bindiga kirar gida guda 26, da kuma bindiga kirar Dane guda 22 da wasu muggan makamai.

Ya kara da cewa Alburushin bindiga kirar AK47 guda 21, sai kuma radio baofeng guda 1, motoci 6 babura 11, kekuna5, wayoyin hannun guda 38 da kuma kudi da sukai miliyan 2.7 da wasu abubuwa na daga cikin wadanda dakarun sojojin suka sami nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’addan.

Ya yankin area maso gabas kuwa dakarun operation Hadin Kai sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’addan 52 tare da kama 40 inda suka sami nasarar kubutar da 14 cikin wadanda suka yi garkuwa da su.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp