Home DUNIYA Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarunta sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda 125, tare da kama 200, inda suka sami nasarar kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su a wasu mabambanta hare hare da suka gudanar a kasar cikin mako daya.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada Labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba ya fitar a ranar juma’a yayin da yake bayar da bayani kan ayyukan rundunar a birnin Abuja.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito Buba na cewa dakarun sun kwato makamai 120, gami da alburusai 1,793, sai kuma bindiga kirar AK47 guda 56, da kuma bindiga kirar gida guda 26, da kuma bindiga kirar Dane guda 22 da wasu muggan makamai.

Ya kara da cewa Alburushin bindiga kirar AK47 guda 21, sai kuma radio baofeng guda 1, motoci 6 babura 11, kekuna5, wayoyin hannun guda 38 da kuma kudi da sukai miliyan 2.7 da wasu abubuwa na daga cikin wadanda dakarun sojojin suka sami nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’addan.

Ya yankin area maso gabas kuwa dakarun operation Hadin Kai sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’addan 52 tare da kama 40 inda suka sami nasarar kubutar da 14 cikin wadanda suka yi garkuwa da su.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp