Home DUNIYA Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Sojojin Nijeirya sun hallaka ‘yan Ta’adda 125 a cikin mako daya -DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarunta sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda 125, tare da kama 200, inda suka sami nasarar kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su a wasu mabambanta hare hare da suka gudanar a kasar cikin mako daya.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada Labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba ya fitar a ranar juma’a yayin da yake bayar da bayani kan ayyukan rundunar a birnin Abuja.

jaridar Emergency Digest ta ruwaito Buba na cewa dakarun sun kwato makamai 120, gami da alburusai 1,793, sai kuma bindiga kirar AK47 guda 56, da kuma bindiga kirar gida guda 26, da kuma bindiga kirar Dane guda 22 da wasu muggan makamai.

Ya kara da cewa Alburushin bindiga kirar AK47 guda 21, sai kuma radio baofeng guda 1, motoci 6 babura 11, kekuna5, wayoyin hannun guda 38 da kuma kudi da sukai miliyan 2.7 da wasu abubuwa na daga cikin wadanda dakarun sojojin suka sami nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’addan.

Ya yankin area maso gabas kuwa dakarun operation Hadin Kai sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’addan 52 tare da kama 40 inda suka sami nasarar kubutar da 14 cikin wadanda suka yi garkuwa da su.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp