Home General Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari ya mayar wa attajirin Afirka Aliko Dangote martani bayan zargin cewa wasu mutanen NNPC sun mallaka kamfanin tace mai a ƙasashen ƙetare.

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X, Mele Kyari ya yi watsi da zargin inda ya ce ba shi da wani kamfani na tace mai a ƙasashen ƙetare.

A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta, Aliko Dangote ya yi zargin cewa wasu ƴankasuwar mai da mutanen NNPC sun buɗe kamfanin tace mai a Malta.

“Mun san inda ake wannan aikin kuma mun san me suke yi, ba wai ba mu sani ba,” in ji Dangote.

Da yake mayar da martani, Shugaban NNPC ya ce “ba ni da wani kasuwanci ko wanda ake yi da sunana a ko’ina a duniya idan ba wanda nake yi ba gida na aikin gona.”

“Sanna ba ni da masaniya ko akwai ma’aikacin NNPC da yake da matata a Malta ko wani wuri a sassan duniya.”

Shugaban na NNPC ya buƙaci a fallasa waɗanda Dangote yake zargi tare da sanar da jami’an tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace da su.

A cikin bidiyon da ke yawo na Dangote, ya yi zargin ana shigo da man da ba ya da inganci a Najeriya, dalilin ya sa wasu ke samun matsaloli a motocinsu, a cewarsa.

Ya ce idan har ana son tabbatar da gaskiyar abin da yake fada – abin da ya kamata a gudanar shi ne gwaji kan man da ake sayarwa a gidajen mai amma ba daga tashar ruwa ba.

“Wani kawai zai shigo da jirgin ruwa ya gabatar da samfuri da takardar bogi sai a sahale masa – nan gaba za mu ci gaba da magana,” in ji Dangote.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp