Home General Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban NNPC ya mayarwa da Dangote Martani

Shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari ya mayar wa attajirin Afirka Aliko Dangote martani bayan zargin cewa wasu mutanen NNPC sun mallaka kamfanin tace mai a ƙasashen ƙetare.

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X, Mele Kyari ya yi watsi da zargin inda ya ce ba shi da wani kamfani na tace mai a ƙasashen ƙetare.

A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta, Aliko Dangote ya yi zargin cewa wasu ƴankasuwar mai da mutanen NNPC sun buɗe kamfanin tace mai a Malta.

“Mun san inda ake wannan aikin kuma mun san me suke yi, ba wai ba mu sani ba,” in ji Dangote.

Da yake mayar da martani, Shugaban NNPC ya ce “ba ni da wani kasuwanci ko wanda ake yi da sunana a ko’ina a duniya idan ba wanda nake yi ba gida na aikin gona.”

“Sanna ba ni da masaniya ko akwai ma’aikacin NNPC da yake da matata a Malta ko wani wuri a sassan duniya.”

Shugaban na NNPC ya buƙaci a fallasa waɗanda Dangote yake zargi tare da sanar da jami’an tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace da su.

A cikin bidiyon da ke yawo na Dangote, ya yi zargin ana shigo da man da ba ya da inganci a Najeriya, dalilin ya sa wasu ke samun matsaloli a motocinsu, a cewarsa.

Ya ce idan har ana son tabbatar da gaskiyar abin da yake fada – abin da ya kamata a gudanar shi ne gwaji kan man da ake sayarwa a gidajen mai amma ba daga tashar ruwa ba.

“Wani kawai zai shigo da jirgin ruwa ya gabatar da samfuri da takardar bogi sai a sahale masa – nan gaba za mu ci gaba da magana,” in ji Dangote.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp