Home General Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya gargaɗi ƴan ƙungiyoyin fararen hula da al’ummar jihar su kauce wa hargitsi a lokacin zanga-zanga da ake shirin gudanarwa daga ɗaya zuwa 10 ga watan Agusta a jihar.

Gwamna Adeleke, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi tare da wasu ‘yan majalisar zartarwa na jihar Osun ya bayar da shawarar ne a wata tattaunawa da mambobin ƙungiyoyin farar hula na jihar a yau Talata.

Gwamnan ya ce duk da cewa ya san ƴan kasa na da ƴancin yin zanga-zanga, su tabbatar da cewa ba su saka rayuwar ƴan jihar cikin haɗari ba.

Gwamnan ya ce “kwanciyar hankali da lafiyar ƴan jihar Osun shi ne babban damuwarmu da abin da muka fi mayar da hankali a kai a zanga-zangar da ake shirin gudanarwa.”

“Babban burina a matsayin gwamnan wannan jihar shi ne mayar da jihar a matsayin babban misali mai kyau ga sauran jihohi,” in ji gwamnan.

“Saboda haka ne na shawarce ku ƴan jihar Osun da ku kasance masu biyaya ga doka da oda a lokacin zanga-zanga da kuma bayan zanga-zanagar, ba za mu amince da duk wani hargitsi ba da tashin hankali yayin da kuke gudanar da zanga-zanga.” in ji gwamnan.

Ƙungiyoyin fararen hula da sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu na jihar sun yaba wa gwamnan da gudanar da irin wannan tattaunawar inda suka ce sun amince za su yi biyayya ga doka da kuma tabbatar da an yi zanga-zangar cikin lumana.

PRNIgeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp