Home General Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya gargaɗi ƴan ƙungiyoyin fararen hula da al’ummar jihar su kauce wa hargitsi a lokacin zanga-zanga da ake shirin gudanarwa daga ɗaya zuwa 10 ga watan Agusta a jihar.

Gwamna Adeleke, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi tare da wasu ‘yan majalisar zartarwa na jihar Osun ya bayar da shawarar ne a wata tattaunawa da mambobin ƙungiyoyin farar hula na jihar a yau Talata.

Gwamnan ya ce duk da cewa ya san ƴan kasa na da ƴancin yin zanga-zanga, su tabbatar da cewa ba su saka rayuwar ƴan jihar cikin haɗari ba.

Gwamnan ya ce “kwanciyar hankali da lafiyar ƴan jihar Osun shi ne babban damuwarmu da abin da muka fi mayar da hankali a kai a zanga-zangar da ake shirin gudanarwa.”

“Babban burina a matsayin gwamnan wannan jihar shi ne mayar da jihar a matsayin babban misali mai kyau ga sauran jihohi,” in ji gwamnan.

“Saboda haka ne na shawarce ku ƴan jihar Osun da ku kasance masu biyaya ga doka da oda a lokacin zanga-zanga da kuma bayan zanga-zanagar, ba za mu amince da duk wani hargitsi ba da tashin hankali yayin da kuke gudanar da zanga-zanga.” in ji gwamnan.

Ƙungiyoyin fararen hula da sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu na jihar sun yaba wa gwamnan da gudanar da irin wannan tattaunawar inda suka ce sun amince za su yi biyayya ga doka da kuma tabbatar da an yi zanga-zangar cikin lumana.

PRNIgeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp