Home General Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan Osun ya gargadi masu Zanga – Zanga a jihar

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya gargaɗi ƴan ƙungiyoyin fararen hula da al’ummar jihar su kauce wa hargitsi a lokacin zanga-zanga da ake shirin gudanarwa daga ɗaya zuwa 10 ga watan Agusta a jihar.

Gwamna Adeleke, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi tare da wasu ‘yan majalisar zartarwa na jihar Osun ya bayar da shawarar ne a wata tattaunawa da mambobin ƙungiyoyin farar hula na jihar a yau Talata.

Gwamnan ya ce duk da cewa ya san ƴan kasa na da ƴancin yin zanga-zanga, su tabbatar da cewa ba su saka rayuwar ƴan jihar cikin haɗari ba.

Gwamnan ya ce “kwanciyar hankali da lafiyar ƴan jihar Osun shi ne babban damuwarmu da abin da muka fi mayar da hankali a kai a zanga-zangar da ake shirin gudanarwa.”

“Babban burina a matsayin gwamnan wannan jihar shi ne mayar da jihar a matsayin babban misali mai kyau ga sauran jihohi,” in ji gwamnan.

“Saboda haka ne na shawarce ku ƴan jihar Osun da ku kasance masu biyaya ga doka da oda a lokacin zanga-zanga da kuma bayan zanga-zanagar, ba za mu amince da duk wani hargitsi ba da tashin hankali yayin da kuke gudanar da zanga-zanga.” in ji gwamnan.

Ƙungiyoyin fararen hula da sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu na jihar sun yaba wa gwamnan da gudanar da irin wannan tattaunawar inda suka ce sun amince za su yi biyayya ga doka da kuma tabbatar da an yi zanga-zangar cikin lumana.

PRNIgeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp