Home Labarai Ana fargabar ‘yan Sanda sun harbi masu Zanga Zanga a Kano

Ana fargabar ‘yan Sanda sun harbi masu Zanga Zanga a Kano

Masu zanga zanga a jihar Kano sun zargi jami’an tsaro da harbi kan masu mutum biyu a cikin su.

Ta cikin wata ganawa da PRNigeria ta yi da guda cikin masu zanga zangar kwamared Aliyu D. yace sun fito zanga-zangar ta lumana amma wasu cikin jami’an ‘yan sandan dake aiki domin samar da tsaro suka fara harba musu hayaki mai saka hawaye inda daga bisani kuma suka fara harbin su da bindiga.

Aliyu yace muddin aka cigaba da tafiya a haka bau dalilin da saka su koma gida sai gwamnati tayi musu abinda ya kamata, na dawo da tallafin man fetur da magance tsadar rayuwar a fadin Nijeriya.

Yayin da ake ci gaba da zanga-zanga a fadin Najeriya, dubban matasa a jihar Kano sai kara fitowa suke daga unguwanni suna taruwa a kan titin gidan gwamnati.

matasan rike da alluna suna ta furta kalmomin “Ba ma yi” wasu matasan na komawa gida suna sake shiri.

Ana fargabar an harbi mutum uku cikin masu zanga-zangar, Jami’an tsaro kuma a wasu wuraren sun zama yan kallo sannan sun janye motocin su ƙanana.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp