Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da shirinta na sayar wa da ma’aikatan gwamnati buhun shinkafa mai nauyin kilogram 50 ko mai kwano 17, da ta sanar a baya a kan farashi mai rahusa – naira dubu 40.

Ma’aikatar ayyuka na musamman ce ta sanar da haka a wata takarda da ta fitar, ɗauke da sa hannun darektar kula da harkokin jama’a, Aderonke Jaiyesimi, mai kwanan wata, 2 ga watan Agustan 2024.

Sai dai takardar ba ta yi bayani kan dalilin da ya sa aka dakatar da shirin ba, ko ma an soke shi ne gabaɗaya ko kuma zuwa wani lokaci aka ɗage shi.

A shirin da aka sanar tun farko, a ranar 1 ga watan Agusta, 2024 ta wata takarda dama’aikatar da fitar, an buƙaci ma’aikatan gwamnati da ke son sayen shinkafar da su je shafin intanet na ofishin shugaban ma’aikata na tarayya su cike wata takarda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp