Home Labarai Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayya ta dakatar da sayar da shinkafa ga ma’aikatan Gwamnati

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da shirinta na sayar wa da ma’aikatan gwamnati buhun shinkafa mai nauyin kilogram 50 ko mai kwano 17, da ta sanar a baya a kan farashi mai rahusa – naira dubu 40.

Ma’aikatar ayyuka na musamman ce ta sanar da haka a wata takarda da ta fitar, ɗauke da sa hannun darektar kula da harkokin jama’a, Aderonke Jaiyesimi, mai kwanan wata, 2 ga watan Agustan 2024.

Sai dai takardar ba ta yi bayani kan dalilin da ya sa aka dakatar da shirin ba, ko ma an soke shi ne gabaɗaya ko kuma zuwa wani lokaci aka ɗage shi.

A shirin da aka sanar tun farko, a ranar 1 ga watan Agusta, 2024 ta wata takarda dama’aikatar da fitar, an buƙaci ma’aikatan gwamnati da ke son sayen shinkafar da su je shafin intanet na ofishin shugaban ma’aikata na tarayya su cike wata takarda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp