Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarun ta sun sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar Boko haram Abu Rijab da wasu mayakan kungiyar sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai a ranar asabar.

Wannan dai na cikin wata sanarwar da mai Magana da yawun ya wallafa a shafin hukumar na X, wanda yace dakarun sun sami nasarar ne sakamakon wani sumame da suka kai garin Bula Daloye dake karamar hukumar Bama a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Yace wannan nasarar ta samu ne sakamakon mika wuya da mayakan ke cigaba da yi su da iyalan su ga dakarun sojoji, bayan matsa kaimi da dakarun ke yi a maboyar ‘yan ta’addan.

Haka kuma sojojin sun sami nasarar kama wadanda ake zargi da aikata ta’addanci tare kuma da kwato bindigu da alburusai.

“bayan musayar wuta da dakarun mu sukayi da ‘yan ta’adda sun sami nasarar hallaka kwamandan kungiyra boko haram Abu Rijab da kuma mayakan kungiyar guda uku.

“kuma sumamen ya kai ga kwato bindiga kirar AK-47 da kuma wayoyin hannu.

“haka kuma Karin ‘yan ta’adda takwas da iyalansu sun mika wuya a karamar hukumar Gwoza.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp