Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarun ta sun sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar Boko haram Abu Rijab da wasu mayakan kungiyar sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai a ranar asabar.

Wannan dai na cikin wata sanarwar da mai Magana da yawun ya wallafa a shafin hukumar na X, wanda yace dakarun sun sami nasarar ne sakamakon wani sumame da suka kai garin Bula Daloye dake karamar hukumar Bama a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Yace wannan nasarar ta samu ne sakamakon mika wuya da mayakan ke cigaba da yi su da iyalan su ga dakarun sojoji, bayan matsa kaimi da dakarun ke yi a maboyar ‘yan ta’addan.

Haka kuma sojojin sun sami nasarar kama wadanda ake zargi da aikata ta’addanci tare kuma da kwato bindigu da alburusai.

“bayan musayar wuta da dakarun mu sukayi da ‘yan ta’adda sun sami nasarar hallaka kwamandan kungiyra boko haram Abu Rijab da kuma mayakan kungiyar guda uku.

“kuma sumamen ya kai ga kwato bindiga kirar AK-47 da kuma wayoyin hannu.

“haka kuma Karin ‘yan ta’adda takwas da iyalansu sun mika wuya a karamar hukumar Gwoza.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp