Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarun ta sun sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar Boko haram Abu Rijab da wasu mayakan kungiyar sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai a ranar asabar.

Wannan dai na cikin wata sanarwar da mai Magana da yawun ya wallafa a shafin hukumar na X, wanda yace dakarun sun sami nasarar ne sakamakon wani sumame da suka kai garin Bula Daloye dake karamar hukumar Bama a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Yace wannan nasarar ta samu ne sakamakon mika wuya da mayakan ke cigaba da yi su da iyalan su ga dakarun sojoji, bayan matsa kaimi da dakarun ke yi a maboyar ‘yan ta’addan.

Haka kuma sojojin sun sami nasarar kama wadanda ake zargi da aikata ta’addanci tare kuma da kwato bindigu da alburusai.

“bayan musayar wuta da dakarun mu sukayi da ‘yan ta’adda sun sami nasarar hallaka kwamandan kungiyra boko haram Abu Rijab da kuma mayakan kungiyar guda uku.

“kuma sumamen ya kai ga kwato bindiga kirar AK-47 da kuma wayoyin hannu.

“haka kuma Karin ‘yan ta’adda takwas da iyalansu sun mika wuya a karamar hukumar Gwoza.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp