Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Sojojin Nijeriya sun hallaka kwamandan Boko haram, Abu Rijab, a jihar Borno

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarun ta sun sami nasarar hallaka kwamandan mayakan kungiyar Boko haram Abu Rijab da wasu mayakan kungiyar sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai a ranar asabar.

Wannan dai na cikin wata sanarwar da mai Magana da yawun ya wallafa a shafin hukumar na X, wanda yace dakarun sun sami nasarar ne sakamakon wani sumame da suka kai garin Bula Daloye dake karamar hukumar Bama a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Yace wannan nasarar ta samu ne sakamakon mika wuya da mayakan ke cigaba da yi su da iyalan su ga dakarun sojoji, bayan matsa kaimi da dakarun ke yi a maboyar ‘yan ta’addan.

Haka kuma sojojin sun sami nasarar kama wadanda ake zargi da aikata ta’addanci tare kuma da kwato bindigu da alburusai.

“bayan musayar wuta da dakarun mu sukayi da ‘yan ta’adda sun sami nasarar hallaka kwamandan kungiyra boko haram Abu Rijab da kuma mayakan kungiyar guda uku.

“kuma sumamen ya kai ga kwato bindiga kirar AK-47 da kuma wayoyin hannu.

“haka kuma Karin ‘yan ta’adda takwas da iyalansu sun mika wuya a karamar hukumar Gwoza.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp