Home General Gwamnatin Nijeriya ta musanta karin harajin kayayyaki a kasar

Gwamnatin Nijeriya ta musanta karin harajin kayayyaki a kasar

Gwamnatin Nijeriya ta musanta raɗe-raɗin cewa ta ƙara yawan harijin kayayyaki zuwa kashi 10%, daga kashi 7.5%.

Ministan kuɗi na Najeriya, Wale Edun a cikin wata sanarwa ya ce har yanzu dokokin ƙasar sun ƙayyade cewa hariji kayayyakin da ake biya kashi 7.5% ne.

Ya ce: “Harajin kayayyaki a Nijeriya yana nan a kashi 7.5% , kuma hakan gwamnati ke karɓa. Domin haka gwamnati da dukkan hukumomin ta suna biyayya ga wannan tanadi na doka, kuma ba za su saɓa ba.

Rahotan da aka riƙa yaɗawa game da ƙarin harajin kayyakin a Nijeriya ya janyo martani daga ɓangarori da dama, ciki harda na ƴan siyasa.

Tuni dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar kuma ɗan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yi allawadai da matakin.

Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafin sada zumuntansa na X.

Ya bayyana matakin a matsayin wani abu da zai yi mummunar illa ga al’ummar Najeriya, yana mai hasashen cewa hakan zai kara ta’azzara matsalar tsadar rayuwa da ƙasar ke fama da ita da kuma kawo cikas ga ci gaban tattalin arzikin Nijeriya.

“Ƙara kuɗin haraji zai zama wuta mai zafi da za ta cinye ainihin mutanenmu.” in ji Atiku.

“Wannan matakin zai haifar da koma baya da ƙara zurfafa matsalar tsadar rayuwa a cikin gida da kuma ƙara tabarbarewar ci gaban tattalin arzikin ƙasar ne kawai”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp