Home General Gwamnatin Nijeriya ta musanta karin harajin kayayyaki a kasar

Gwamnatin Nijeriya ta musanta karin harajin kayayyaki a kasar

Gwamnatin Nijeriya ta musanta raɗe-raɗin cewa ta ƙara yawan harijin kayayyaki zuwa kashi 10%, daga kashi 7.5%.

Ministan kuɗi na Najeriya, Wale Edun a cikin wata sanarwa ya ce har yanzu dokokin ƙasar sun ƙayyade cewa hariji kayayyakin da ake biya kashi 7.5% ne.

Ya ce: “Harajin kayayyaki a Nijeriya yana nan a kashi 7.5% , kuma hakan gwamnati ke karɓa. Domin haka gwamnati da dukkan hukumomin ta suna biyayya ga wannan tanadi na doka, kuma ba za su saɓa ba.

Rahotan da aka riƙa yaɗawa game da ƙarin harajin kayyakin a Nijeriya ya janyo martani daga ɓangarori da dama, ciki harda na ƴan siyasa.

Tuni dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar kuma ɗan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya yi allawadai da matakin.

Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafin sada zumuntansa na X.

Ya bayyana matakin a matsayin wani abu da zai yi mummunar illa ga al’ummar Najeriya, yana mai hasashen cewa hakan zai kara ta’azzara matsalar tsadar rayuwa da ƙasar ke fama da ita da kuma kawo cikas ga ci gaban tattalin arzikin Nijeriya.

“Ƙara kuɗin haraji zai zama wuta mai zafi da za ta cinye ainihin mutanenmu.” in ji Atiku.

“Wannan matakin zai haifar da koma baya da ƙara zurfafa matsalar tsadar rayuwa a cikin gida da kuma ƙara tabarbarewar ci gaban tattalin arzikin ƙasar ne kawai”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp