Rahotannin daga birnin tarayya Abuja na tabbatar da cewa jami’an hukumar Tsaro ta DSS sun mamaye ofishin kungiyar SERAP da ke birnin.
wannan dai na zuwa ne bayan da jami’an suka kama shugabn kungiyar kwadago ta kasa Joe Ajero.
Read Also:
Rahotannin sun nuna cewa jami’an sun nemi ganawa da shugabannin kungiyar kare hakkin dan Adam da lura da al’amuran tattalin arziki.
A cikin wani rubutu da aka wallafa a shafin X na SERAP, an bayyana cewa jami’an DSS sun mamaye ofishinsu ba bisa ka’ida ba.
Kungiyar ta bukaci Shugaban kasa Tinubu da ya gaggauta umartar DSS da ta daina tsoratarwa da cin zarafin ‘yan Najeriya.











