Home General Ƙarin farashin mai a Najeriya ya sa albashi mafi ƙaranci na 70,000...

Ƙarin farashin mai a Najeriya ya sa albashi mafi ƙaranci na 70,000 ba shi da amfani – NLC

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya, NLC ta ce za ta sake komawa ga gwamnatin tarayya domin ta ji yadda ma’aikata za su rayu bayan sake kara farashin man fetur a kasar.

Kungiyar ta kwadago ta bayyana hakan a ranar Alhamis in da ta ce farashin mai a yanzu haka ya riga ya haɗiye sabon tsarin albashin da gwamnati ta yi alƙawarin bayarwa na naira dubu 70 wanda kuma har yanzu ba a fara bayarwa ba.

Shugaban ƙungiyar ta NLC, Kwamared Joe Ajaero wanda ya bayyana hakan yayin buɗe wani taron ƙarawa juna sani a Legas ya ce gwamnati ta yaudare su ta hanyar amince wa da naira 70,000 ɗin a matsayin albashi mafi ƙaƙanta.

Ya kuma shawarci gwamnati da ta magance matsalar yunwa da talauci da damuwar da ƴan Najeriya ke fama da ita tun kafin al’amura su fi ƙarfinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp