Home General EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Tababa da rashin tabbas sun mamaye ziyarar hukumar EFCC da tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello yace ya yi domin amsa tambayoyi dangane da zarge zargen da ake masa na rub da ciki da kudaden talakawa da kuma halarta kudaden haramun.

Yayin da tsohon gwamnan ta hannun mai magana da yawunsa Ohiare Michael ya ce yau ya kai kansa EFCC tare da rakiyar lauyoyinsa da kuma gwamnan Kogi Usman Ododo, Hukumar EFCC ta fitar da sanarwar watsi da ikrarin da kuma bayyana cewar har yanzu ta na neman shi ruwa a jallo.

Bello ya shaida wa manema labarai cewar bayan ziyarar domin amsa tambayoyi EFCC ta ce masa ya tafi gida ba tare da masa tambayoyi akan zargin karkata kudaden da suka kai naira biliyan 80 ba.

Tsohon gwamnan ya bukaci hukumar yaki da cin hancin ta ci gaba da aiki da dokokin da suka samar da ita tare da mutunta ‘yancin jama’ar kasa, ya yin da ya kara da cewar matakan da ya dauka na kin amsa gayyatar hukumar ya yi su ne domin kare hakkokinsa.

Sai dai mai magana da yawun EFCCn Dele Oyewale ya ce babu gaskiya dangane da mika wuyar tsohon gwamnan, kuma har yanzu suna neman sa ruwa a jallo.

Ko da yake a safiyar Alhamis, jami’an hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati na EFCC sun zagayi gidan da ake zargin Yahaya Bello na ciki, wanda suke bukatar ya mika kansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp