Home AFIRKA Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da...

Harin masu tada kayar baya a Mali ya kashe mutum 70 da jikkata wasu 200

Wani harin mayaƙa masu iƙirarin jihadi da aka kai sansanin horar da sojoji da filin tashi da saukar jiragen sama na babba birnin Mali, Bamako ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 70 tare da jikkata 200, adadi mafi muni na jami’an tsaro da aka taɓa samu a shekarun baya-bayann nan.

Wata majiyar tsaro da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa mutanee 77 ne suka mutu, kana 255 suka samu raunuka a harin da aka kai Bamako a ranar Talata.

Zalika, wani bayanin sirri na hukuma da aka tantance sahihancinsa ya ce adadin waɗanda suka mutu ya kai kimanin ɗari, inda ya bayyana sunayen 81 daga cikin su.

Jaridar Le Soir da ake wallafawa a kasar ta ranar Alhamis ɗin nan ya ruwaito cewa a ranar aka yi jana’izar kimanin dakaru masu karɓar soji kimanin 50.

Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto mahukuntann gwamnatin sojin Mali ba su fitar da ainihin adadin waɗanda su ka mutu  a harin da ƙungiyar mayaƙa masu iƙirarin jihadi da ke da alaƙa da Al-Qaeda ta ɗauki alhakin kai wa ba.

Ƙwararru sun ce harin sshi ne naa farko irin sa a cikin shekaru, kuma ta yi mummmunan tasiri a kan gwamnatin sojin ƙasar.

Ba a cika samun hare-hare a babban birnin ƙasar Mali  kamar yadda ake samu a sauran sassan ƙasar kusan kullayaumin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp