Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasar a safiyar yau Asabar.
Lamarin da ya jefa miliyoyin mutane a jihohi da dama cikin duhu.
Wannan dai shi ne karo na uku da babban layin wutar ke lalacewa cikin mako ɗaya, kuma na takwas tun soma wannan shekara.
Read Also:
Bayanai daga aka tattara sun nuna cewa babu ko megawatt ɗaya a babban layin zuwa safiyar Asabar ɗin nan.
Masana kan harkar wutar lantarki dai sun yi kira da a sabunta kayayakin babbar cibiyar wutar lantaki ta ƙasar.
Sun ce yawan katsewar wutar lantarkin da ake fuskanta na da alaƙa ne da rashin sauya kayyakin babbar cibiyar wutar lantakin ƙasar.












