Home Labarai Mutum 10 sun mutu, yayin da bakwai suka jikkata bayan rushewar gini...

Mutum 10 sun mutu, yayin da bakwai suka jikkata bayan rushewar gini a Ibadan

Aƙalla mutum 10 ne suka mutu yayainwa su bakwai suka jikkata bayan faɗuwar gini a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Cikin wata sanarwa da hukumar kashe gobara ta jihar ta fitar, ta ce lamarin ya faru da tsakar daren da ya gabata a unguwar Jegeda Oluloyo da ke binrin na Ibadan, kamar yadda Jaridar unch ya ruwaito.

Sanarwar ta ƙara da cewa yayin da aka zaƙulo gawarwarkin mutum 10 daga cikin ɓaraguzan ginin, an kuma ceto wasu mutum bakwai da raunuka, sannan an ci gaba da aikin ceton domin nemo ƙarin mutane.

Faɗuwar gine-gine dai wani lamari ne da ke neman zaman ruwan dare a Najeriya, inda da dama takan zo da asarar rayuka masu yawa.

Mahukuntar ƙasar na ɗora alhakin matsalar kan rashin bin ingantaccen tsari da ƙa’ida a lokacin yin gine-ginen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp