Home General Gwamnatin Najeriya ta kwace kwangilar hanyar Abuja-Kaduna daga hannun kamfanin Julius Berger

Gwamnatin Najeriya ta kwace kwangilar hanyar Abuja-Kaduna daga hannun kamfanin Julius Berger

Gwamnatin Najeriya ta sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar aikin hanyar da ta tashi daga Abuja zuwa Kaduna da ta ƙulla da kamfanin Julius Berger.

Bayan cikar wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin ta baiwa kamfanin na ɗaukar mataki kan tafiyar wahainiya da aikin ke yi, a yanzu ta sanar da ficewa daga yarjejeniyar ba tare da samun damar yin wata tattaunawa ba.

Ta cikin sanarwar da ma’aikatar ayyukan ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta Mohammed Ahmed ta ce an shafe watanni 13 a jere ana tattaunawa da kamfanin amma an kasa cimma matsaya, don haka babu wani zabi da ya wuce kawo ƙarshen yarjejeniyar.

Baya ga  tafiyar wahainiya da aikin ke yi, ana kuma zargin sa da ƙin bada cikakken bayani kan kuɗin da aikin ya laƙume kawo yanzu, ƙin biyayya ga dokokin da aka shimfida, da kuma ƙin biyayya ga shawarwarin da ma’aikatar ayyuka ta bashi.

RFI ta ruwaito cewa an shafe tsahon watanni ana yamutsa gashin baki tsakanin kamfani da gwamnati kan waɗannan matsaloli da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp