Home General Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun siyasa da ‘yan takara sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya.

An yi bikin sanya hannun ne ƙarƙashin jagorancin kwamitin zaman lafiya na ƙasa NPC, a cibiyar raya al’adu da ke Akure, babban birni jihar.

Shugaban kwamitin, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya yi kira ga duka masu ruwa da tsaki su tabbatar an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali.

Ya kuma buƙaci shugabannin jam’iyyu da ‘yan takara su amince da sakamakon zaɓen matsawar an gudanar da shi cikin kwanciyar hankali da lumana.

A nasa ɓangare shugaban hukumar zaɓen kasar, Farfesa Mahmood Yakubu ya yaba wa kwamitin bisa ƙoƙarinsa na haɗa kan jam’iyyun da ‘yan takara a teburin yarjejeniyar zaman lafiya a lokutan zaɓukan ƙasar.

Farfesa Yakubu ya kuma yi kira ga shugabannin addinai da sarakuna da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa hannu da hukumarsa don gudanar da zaɓen gwamnan jihar cikin kwanciyar hankali da lumana.

A ranar 16 ga watan Nuwamban da muke ciki ne za a gudanar da zaɓen gwamnan jihar ta Ondo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp