Home General Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Gwamnatin jihar Kano ta ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi aiki kwashe yaran da ke gararamba a titunan birnin.

Hukumomi sun ce ɗaukar matakin ya zama wajibi kasancewar barin yara ƙanana suna yawo a tituna babbar barazana ce ga tsaro da kuma ci gaba al’umma.

Kwamitin zai kuma bai wa gwamnati shawarar kan yadda za a mayar da yaran garuruwan da suka fito.

Kwamitin ƙarkashin shugabancin kwamandan hukumar Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa zai bi diddigi tare da zaƙulo yaran da suke yawo a kwararo da tituna suna kwana a kasuwanni da ƙarƙashin gada a sassan birnin Kano domin samar musu da kyakkyawar makoma da kuma maslahar al’umma.

“Yaran da za mu fara kamawa sune waɗanda suke kamar an zubar da su yawo kan titi, waɗanda ba su da wata makoma, mafi yawansu ba a san daga inda suke ba. Waɗansu ‘yan Kano ne wasu yan wasu jihohin wasu kuma ‘yan wajen ƙasar nan ne ma,” in ji Ɗaurawa

“Wasunsu rayuwa ce ta yi musu tsauri ta gagara suka koma kwana ƙarƙashin gada da gareji da wajen tuburan masu shayi. Irin waɗannan yaran mai girma gwamna ke fatan a kama a tantance na gida da na wajen a san matakin da za a ɗauka a kansu.

“A basu tarbiyya a mayar da su cikin al’umma domin su zama masu amfani ka da su zama barazana ga al’umma,” in ji Malam Aminu Daurawa.

Wannan kwamitin dai ya ƙunshi wasu ƙananan kwamitoci waɗanda za su yi aikin tantance yaran ta fuskar lafiya da sauran bayanai.

Sheik Daurawa ya ce ba za a faɗi yaushe za a fara wannan aiki ba domin ka da waɗanda ake son a taimakawa su tsere a gaza cimma manufar aikin.

“An bamu filin sansanin alhazai da ke kusa da filin jirgin sama, a nan za mu ajiye su tsawon makonni biyu mu tantance su da lafiyarsu da kuma garuruwansu.

“Za a yi aikin nan ne ƙarƙashin kwamiti guda huɗu da za su kammala aikinsu cikin kwana 14 sannan gwamna ya bayyana mataki na gaba,” in ji Malam Aminu Daurawa.

To sai dai ‘yan kungiyoyin da ake aikin kare kananan yara na ganin akwai bukatar gwamnati ta lura da wasu mahimman abubuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp