Home General Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Dalilin Gwamnatin Kano na fara kamen kananan yaran dake yawo a titi

Gwamnatin jihar Kano ta ƙaddamar da wani kwamiti da zai yi aiki kwashe yaran da ke gararamba a titunan birnin.

Hukumomi sun ce ɗaukar matakin ya zama wajibi kasancewar barin yara ƙanana suna yawo a tituna babbar barazana ce ga tsaro da kuma ci gaba al’umma.

Kwamitin zai kuma bai wa gwamnati shawarar kan yadda za a mayar da yaran garuruwan da suka fito.

Kwamitin ƙarkashin shugabancin kwamandan hukumar Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa zai bi diddigi tare da zaƙulo yaran da suke yawo a kwararo da tituna suna kwana a kasuwanni da ƙarƙashin gada a sassan birnin Kano domin samar musu da kyakkyawar makoma da kuma maslahar al’umma.

“Yaran da za mu fara kamawa sune waɗanda suke kamar an zubar da su yawo kan titi, waɗanda ba su da wata makoma, mafi yawansu ba a san daga inda suke ba. Waɗansu ‘yan Kano ne wasu yan wasu jihohin wasu kuma ‘yan wajen ƙasar nan ne ma,” in ji Ɗaurawa

“Wasunsu rayuwa ce ta yi musu tsauri ta gagara suka koma kwana ƙarƙashin gada da gareji da wajen tuburan masu shayi. Irin waɗannan yaran mai girma gwamna ke fatan a kama a tantance na gida da na wajen a san matakin da za a ɗauka a kansu.

“A basu tarbiyya a mayar da su cikin al’umma domin su zama masu amfani ka da su zama barazana ga al’umma,” in ji Malam Aminu Daurawa.

Wannan kwamitin dai ya ƙunshi wasu ƙananan kwamitoci waɗanda za su yi aikin tantance yaran ta fuskar lafiya da sauran bayanai.

Sheik Daurawa ya ce ba za a faɗi yaushe za a fara wannan aiki ba domin ka da waɗanda ake son a taimakawa su tsere a gaza cimma manufar aikin.

“An bamu filin sansanin alhazai da ke kusa da filin jirgin sama, a nan za mu ajiye su tsawon makonni biyu mu tantance su da lafiyarsu da kuma garuruwansu.

“Za a yi aikin nan ne ƙarƙashin kwamiti guda huɗu da za su kammala aikinsu cikin kwana 14 sannan gwamna ya bayyana mataki na gaba,” in ji Malam Aminu Daurawa.

To sai dai ‘yan kungiyoyin da ake aikin kare kananan yara na ganin akwai bukatar gwamnati ta lura da wasu mahimman abubuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp