Home General Hukumar EFCC ta ce ta yi nasarar kama Yahaya Bello

Hukumar EFCC ta ce ta yi nasarar kama Yahaya Bello

Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzƙin Najeriya ta’annati, EFCC, ta ce ta kama tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, a yau Talata.

Kafin hukumar ta tabbatar da kama shi rahotanni da dama na ambato cewa, tsohon gwamnan wanda ke fuskantar tuhumar almundahana, ya kai kansa ne ofishin hukumar da ke Abuja tare da rakiyar wasu lauyoyinsa.

A wani hoton bidiyo na tashar talabijin ta Channels, kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da cewa hukumar tana tsare da tsohon gwamnan na Kogi.

Taƙaddama ta kasance tsakanin EFCC da tsohon gwamnan, bayan da hukumar ta ayyana nemansa a watan Afirilu, bayan ya ƙi amsa gayyatar da ta sha aika masa tare da nuna tirjiya kan duk wani yunƙuri na kama shi, wanda hakan ya sa ya shiga kulli-kurciya da hukumar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp