Home General Tinubu na ganawa da shugaban Faransa a birnin Paris

Tinubu na ganawa da shugaban Faransa a birnin Paris

Shugaban Najeriya na yin wata ganawa da shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron a ranar farko ta ziyarar aiki da shugaban na Najeriya ke yi a ƙasar.

A yau Alhamis, Tinubu ya isa fadar shugaban Faransa ta Elysee tare da tawagarsa, wadda ta hada da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tugga da ministan kuɗi, Wale Edun da na tsaro Badaru Abubakar.

A ɓangare ɗaya shugaban Faransa ya shiga ɗakin taron ne tare da ƙaramin ministan harkokin waje na ƙasar, Thani Mohamed Soilihi da kuma ministan tsaro na Faransa, Sebastien Lecornu da sauran jami’ai.

Ana sa ran Najeriya da Faransa za su ƙulla hulɗoɗi na diflomasiyya da kasuwanci a lokacin ziyarar ta shugaba Tinubu, wadda take zuwa bayan ragin tagomashi da Faransa take samu a Afirka.

Dangantaka ta yi tsami tsakanin Faransa da ƙasashen da ta rena a yammacin Afirka, kamar Nijar da Burkin Faso da Mali.

Ƙasashen sun yanke huldar diflomasiyya da Yamma tare da karkata akalarsu zuwa ɓangaren Rasha.

A matsayinsa na shugaban ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka, Tinubu ya yi ƙoƙarin ganin ƙasashen Nijar da Mali da Bukina Faso sun koma tafarkin dimokuraɗiyya sai dai har yanzu abin ya ci tura.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp