Home General Gwamnatin Katsina ta amince da naira 70,000 mafi ƙanƙantar albashi a jihar

Gwamnatin Katsina ta amince da naira 70,000 mafi ƙanƙantar albashi a jihar

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ya amince da naira 70,000 a matsayin mafi ƙanƙantar albashi ga ma’aikata jihar.

Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce amincewar ta ƙunshi sake fasalin albashin ma’aikatan jihar ciki har da na ƙananan hukumomi da malaman makaranta.

Dikko Radda ya ce sabon albashin zai fara aiki daga watan Disamba mai kamawa.

”Ina miƙa godiya da jinjina ga ma’aikatan jihar Katsina bisa haƙuri da jajircewa da suka nuna, kuma ina kira a gare da ku ƙara jajircewa wajen aiki bisa gaskiya da riƙon amana…”, in ji gwamnan na Katsina.

A ranar Juma’a ne ƙungiyar NLC ta yi barazanar fara yajin aiki a wasu jihohin ƙasar ranar Litinin, ciki har da Katsina, saboda rashin amincewa da sabon tsarin albashin a jihohin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp