Home General Gwamnatin Katsina ta amince da naira 70,000 mafi ƙanƙantar albashi a jihar

Gwamnatin Katsina ta amince da naira 70,000 mafi ƙanƙantar albashi a jihar

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ya amince da naira 70,000 a matsayin mafi ƙanƙantar albashi ga ma’aikata jihar.

Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce amincewar ta ƙunshi sake fasalin albashin ma’aikatan jihar ciki har da na ƙananan hukumomi da malaman makaranta.

Dikko Radda ya ce sabon albashin zai fara aiki daga watan Disamba mai kamawa.

”Ina miƙa godiya da jinjina ga ma’aikatan jihar Katsina bisa haƙuri da jajircewa da suka nuna, kuma ina kira a gare da ku ƙara jajircewa wajen aiki bisa gaskiya da riƙon amana…”, in ji gwamnan na Katsina.

A ranar Juma’a ne ƙungiyar NLC ta yi barazanar fara yajin aiki a wasu jihohin ƙasar ranar Litinin, ciki har da Katsina, saboda rashin amincewa da sabon tsarin albashin a jihohin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp