Home General Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya – shugabar Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, (WTO) Dakta Ngozi Okonjo-Iweala – murnar sake zaɓarta a muƙamin a wa’adin mulki na biyu.

A ranar Juma’a ne aka sake zaɓar Dakta Ngozi a matsayin shugabar WTO a wa’adin mulki na biyu.

Cikin wata sanarwar da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya ce ya yi farin ciki da yadda ƙasashe mambobin WTO suka amince wa Ms Okonjo-Iweala ta zarce a karo na biyu na shugabancin WTO.

”Hakan ya nuna irin ƙwarin gwiwa da amincewa da duniya ta yi da jagorancinta, tare da cike da fatan ƙarfafa da bunƙasa kasuwancin duniya”, in ji Tinubu.

A shekarar 2021 ne tsohuwar ministar ta Najeriya – wanda kuma fitacciyar masaniyar tattalin arziki da kuɗaɗe ce – ta kafa ta tarihin zama ‘yar Afirka ta farko kuma mace ta farko da ta taɓa jarogantar ƙungiyar WTO mai mambobin ƙasashe 164 a faɗin duniya.

Wa’adin mulkinta na farko a matsayin shugabar WTO ta bakwai zai ƙare ranar 31 ga watan Agustan 2025, yayin da wa’adinta na biyu zai ƙare a shekarar 2029.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp