Home General Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya – shugabar Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, (WTO) Dakta Ngozi Okonjo-Iweala – murnar sake zaɓarta a muƙamin a wa’adin mulki na biyu.

A ranar Juma’a ne aka sake zaɓar Dakta Ngozi a matsayin shugabar WTO a wa’adin mulki na biyu.

Cikin wata sanarwar da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya ce ya yi farin ciki da yadda ƙasashe mambobin WTO suka amince wa Ms Okonjo-Iweala ta zarce a karo na biyu na shugabancin WTO.

”Hakan ya nuna irin ƙwarin gwiwa da amincewa da duniya ta yi da jagorancinta, tare da cike da fatan ƙarfafa da bunƙasa kasuwancin duniya”, in ji Tinubu.

A shekarar 2021 ne tsohuwar ministar ta Najeriya – wanda kuma fitacciyar masaniyar tattalin arziki da kuɗaɗe ce – ta kafa ta tarihin zama ‘yar Afirka ta farko kuma mace ta farko da ta taɓa jarogantar ƙungiyar WTO mai mambobin ƙasashe 164 a faɗin duniya.

Wa’adin mulkinta na farko a matsayin shugabar WTO ta bakwai zai ƙare ranar 31 ga watan Agustan 2025, yayin da wa’adinta na biyu zai ƙare a shekarar 2029.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp