Home General Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Tinubu ya yaba da sake zaɓar Ngozi shugabar WTO

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya taya – shugabar Ƙungiyar Cinikayya ta Duniya, (WTO) Dakta Ngozi Okonjo-Iweala – murnar sake zaɓarta a muƙamin a wa’adin mulki na biyu.

A ranar Juma’a ne aka sake zaɓar Dakta Ngozi a matsayin shugabar WTO a wa’adin mulki na biyu.

Cikin wata sanarwar da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya ce ya yi farin ciki da yadda ƙasashe mambobin WTO suka amince wa Ms Okonjo-Iweala ta zarce a karo na biyu na shugabancin WTO.

”Hakan ya nuna irin ƙwarin gwiwa da amincewa da duniya ta yi da jagorancinta, tare da cike da fatan ƙarfafa da bunƙasa kasuwancin duniya”, in ji Tinubu.

A shekarar 2021 ne tsohuwar ministar ta Najeriya – wanda kuma fitacciyar masaniyar tattalin arziki da kuɗaɗe ce – ta kafa ta tarihin zama ‘yar Afirka ta farko kuma mace ta farko da ta taɓa jarogantar ƙungiyar WTO mai mambobin ƙasashe 164 a faɗin duniya.

Wa’adin mulkinta na farko a matsayin shugabar WTO ta bakwai zai ƙare ranar 31 ga watan Agustan 2025, yayin da wa’adinta na biyu zai ƙare a shekarar 2029.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp