Home General Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar Dattijai Ta amince da dokar haramta fitar da Masara daga Nijeriya

Majalisar DattawaN Nigeriya ta amince da gyaran dokar da ta haramta fitar da tsabar masara (wadda ba a sarrafa ba), inda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga waɗanda suka karya wannan doka.

Dokar, wadda ta samo asali daga Majalisar Wakilai, tana nufin hana fitar da masara mai yawa, musamman wadda ta kai ko ta haura ton ɗaya.

Ta kuma tanadi tara mai tsada daidai da kimar kayan da aka fitar ko ɗaurin shekara guda ko kuma haɗa hukuncin biyu ga waɗanda suka keta wannan doka.

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC dake wakiltar alúmmar Ekiti ta tsakiya, yayin gabatar da dokar, ya bayyana muhimmancinta wajen magance matsalar ƙarancin abinci a Najeriya.

“Wannan doka mai sauƙi ce kuma an bi dukkan matakan doka da suka dace wajen nazarinta. Ina roƙon abokan aikina su goyi bayanta,” in ji shi.

Sanata Garba Maidoki (PDP, Kebbi South) ya gabatar da gyara don cire abubuwan da ake sarrafawa daga masara, kamar garin masara da man ganye, domin kare amfanin manoma da masana’antun cikin gida.

Gyaran ya sami amincewa bayan ƙuri’ar jin ra’ayin bakunan ‘yan majalisar.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, wanda ya jagoranci zaman, ya ce barin abubuwan da ake sarrafawa daga masara zai taimaka wajen ƙirƙirar ayyukan yi.

“Waɗannan abubuwan suna da matuƙar muhimmanci wajen samar da ayyukan yi. Cire su ya dace da manufofin tattalin arziƙinmu,” in ji Jibrin.

Dokar da aka gyara za ta ci gaba zuwa kwamitin sulhu don daidaita bambance-bambance tsakanin Majalisar Dattawa da ta Wakilai kafin a miƙa ta ga shugaban ƙasa don rattaba hannu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp