Home General Zamu samar da cibiyar hada kayan aikin CNG a Jihar Kogi –...

Zamu samar da cibiyar hada kayan aikin CNG a Jihar Kogi – FG

Najeriya ta samu gagarumin ci gaba wajen haɓaka cibiyoyin sauya motoci zuwa na amfani da gas ɗin CNG, daga bakwai a 2023 zuwa 158 a 2024 – ƙaruwar da ta kai kaso 2000%.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gas ɗin CNG, Injiniya Michael Oluwagbemi, ya bayyana hakan a taron Nigerian Content karo na 13 a jihar Bayelsa.

Ya bayyana shirin faɗaɗa cibiyoyin zuwa sama da 1,000 don biyan buƙatun masu amfani da ababen hawa.

“Manufar ita ce sauya motoci daga amfani da man fetur zuwa gas ɗin CNG, don ƙirƙirar kasuwar da za ta tallafa wa tashoshin sayar da gas,” in ji shi.

Ya bayyana cewa farashin sauya mota ɗaya yana kusan Naira miliyan ɗaya, kuma akwai damar kasuwa ta Naira tiriliyan 5 don sauya motoci miliyan biyar a Najeriya.

An kuma shirya kafa cibiyar ƙera kayan aikin CNG a Ajaokuta, jihar Kogi.

Shirin ya haɗa da gina ƙarfin aiki, tare da kafa cibiyoyin bayar da horo 1,000 don tabbatar da gyaran motoci a cikin gida.

An fara amfani da kayan gas masu ɗaukar nauyi da aka samo daga fasahar Indiya don magance matsalolin gine-gine.

Oluwagbemi ya jaddada haɗin kai tare da hukumomi don tabbatar da shigar da gas ɗin CNG cikin tsarin makamashi na ƙasa.

“Muna gina tsarin tattalin arziki da zai rage dogaro da man fetur,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Muna da filin hekta 10 kuma muna da niyyar ƙera manyan abubuwan kayan aikin a cikin gida ta hanyar nazarin fasaha,”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp