Home General Zamu samar da cibiyar hada kayan aikin CNG a Jihar Kogi –...

Zamu samar da cibiyar hada kayan aikin CNG a Jihar Kogi – FG

Najeriya ta samu gagarumin ci gaba wajen haɓaka cibiyoyin sauya motoci zuwa na amfani da gas ɗin CNG, daga bakwai a 2023 zuwa 158 a 2024 – ƙaruwar da ta kai kaso 2000%.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gas ɗin CNG, Injiniya Michael Oluwagbemi, ya bayyana hakan a taron Nigerian Content karo na 13 a jihar Bayelsa.

Ya bayyana shirin faɗaɗa cibiyoyin zuwa sama da 1,000 don biyan buƙatun masu amfani da ababen hawa.

“Manufar ita ce sauya motoci daga amfani da man fetur zuwa gas ɗin CNG, don ƙirƙirar kasuwar da za ta tallafa wa tashoshin sayar da gas,” in ji shi.

Ya bayyana cewa farashin sauya mota ɗaya yana kusan Naira miliyan ɗaya, kuma akwai damar kasuwa ta Naira tiriliyan 5 don sauya motoci miliyan biyar a Najeriya.

An kuma shirya kafa cibiyar ƙera kayan aikin CNG a Ajaokuta, jihar Kogi.

Shirin ya haɗa da gina ƙarfin aiki, tare da kafa cibiyoyin bayar da horo 1,000 don tabbatar da gyaran motoci a cikin gida.

An fara amfani da kayan gas masu ɗaukar nauyi da aka samo daga fasahar Indiya don magance matsalolin gine-gine.

Oluwagbemi ya jaddada haɗin kai tare da hukumomi don tabbatar da shigar da gas ɗin CNG cikin tsarin makamashi na ƙasa.

“Muna gina tsarin tattalin arziki da zai rage dogaro da man fetur,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Muna da filin hekta 10 kuma muna da niyyar ƙera manyan abubuwan kayan aikin a cikin gida ta hanyar nazarin fasaha,”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp