Home General Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gwale, Abubakar Muazu Mojo ya yi barazanar ajiye aikinsa na shugabancin karamar hukumar muddin ba’a sauya masa Daraktan Mulki, DPM, na karamar hukumar ba.
jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa tuni dai Shugaban karamar hukumar ta Gwale ya bada umarnin a rufe ofishin DPM din, Danjuma Zubairu Bebeji.
A wani sakon murya da Mojo ya aikewa manema labarai, ya yi ikirarin cewa idan har Daraktan Mulkin bai bar karamar hukumar ba to shi zai bar masa wajen.
Ya kara dacewa manufofin Daraktan Mulkin sun saɓa da tsarin Kwankwasiyya na yi wa jama’a hidima da taimako.
Rahotanni sun baiyana cewa Mojo da DPM ɗin sun jima su na takun saƙa tun lokacin da ya ke Shugaban riko na karamar hukumar ta Gwale kafin a zabe shi a watan Oktoba.
Daga cikin zarge-zargen da Mojo ke yi wa Bebeji har da yi wa karamar hukumar zagon kasa da hana tafiyar da aiki yadda ya kamata, gami da sakaci a wajen aikinsa da hakan ya janyo wasu mahimman takardu su ka ɓata.
Saboda haka ne shugaban karamar hukumar ya ce idan ba a ɗauke Bebeji ba, to shi da majalisar kansilolin sa za su sauka su bar masa wajen.
Sai dai kuma har yanzu ba a ji ta bakin DPM ɗin ba.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp