Home General Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Sabon shugaban ƙaramar hukumar Gwale, Mojo, ya yi barazanar sauka daga kujerarsa

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gwale, Abubakar Muazu Mojo ya yi barazanar ajiye aikinsa na shugabancin karamar hukumar muddin ba’a sauya masa Daraktan Mulki, DPM, na karamar hukumar ba.
jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa tuni dai Shugaban karamar hukumar ta Gwale ya bada umarnin a rufe ofishin DPM din, Danjuma Zubairu Bebeji.
A wani sakon murya da Mojo ya aikewa manema labarai, ya yi ikirarin cewa idan har Daraktan Mulkin bai bar karamar hukumar ba to shi zai bar masa wajen.
Ya kara dacewa manufofin Daraktan Mulkin sun saɓa da tsarin Kwankwasiyya na yi wa jama’a hidima da taimako.
Rahotanni sun baiyana cewa Mojo da DPM ɗin sun jima su na takun saƙa tun lokacin da ya ke Shugaban riko na karamar hukumar ta Gwale kafin a zabe shi a watan Oktoba.
Daga cikin zarge-zargen da Mojo ke yi wa Bebeji har da yi wa karamar hukumar zagon kasa da hana tafiyar da aiki yadda ya kamata, gami da sakaci a wajen aikinsa da hakan ya janyo wasu mahimman takardu su ka ɓata.
Saboda haka ne shugaban karamar hukumar ya ce idan ba a ɗauke Bebeji ba, to shi da majalisar kansilolin sa za su sauka su bar masa wajen.
Sai dai kuma har yanzu ba a ji ta bakin DPM ɗin ba.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp