Babban Hafsan Hafsoshin Sojoin Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa ƴan ta’addan Boko Haram 129,417 da iyalansu sun mika wuya ga jami’an tsaro tsakanin ranar 10 ga watan Yuli zuwa 9 ga watan Disamban wannan shekara ta 2024.
Babbabn hafsan rundunar sojin ƙasa na Najeriya ya bayyana haka ne a taron tsaro na Afrika karo na 18 da ke gudana a birnin Doha na ƙasar Qatar.
Read Also:
Taron, mai taken: “Haɓaka tsaro don samar da Zaman Lafiya wanda Mista Patrick Agbambu na ƙungiyar Watch Africa Initiative ya shirya, ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro daga ƙasashen Najeriya da Guinea Bissau da Gambia da Afirka ta Kudu da Kenya da kuma Qatar.
Janar Musa a jawabinsa ya bayyana cewa alkaluman sun hada da mayaka 30,426, mata 36,774, da yara 62,265.
A cewarsa, wannan nasara ta nuna ci gaban da ake samu wajen samun zaman lafiya a tsakanin al’umma da ke bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.











