Home General Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya...

Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya cikin watanni 6

Babban Hafsan Hafsoshin Sojoin Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa ƴan ta’addan Boko Haram 129,417 da iyalansu sun mika wuya ga jami’an tsaro tsakanin ranar 10 ga watan Yuli zuwa 9 ga watan Disamban wannan shekara ta 2024.

Babbabn hafsan rundunar sojin ƙasa na Najeriya ya bayyana haka ne a taron tsaro na Afrika karo na 18 da ke gudana a birnin Doha na ƙasar Qatar.

Taron, mai taken: “Haɓaka tsaro don samar da Zaman Lafiya wanda Mista Patrick Agbambu na ƙungiyar Watch Africa Initiative ya shirya, ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro daga ƙasashen Najeriya da Guinea Bissau da Gambia da Afirka ta Kudu da Kenya da kuma Qatar.

Janar Musa a jawabinsa ya bayyana cewa alkaluman sun hada da mayaka 30,426, mata 36,774, da yara 62,265.

A cewarsa, wannan nasara ta nuna ci gaban da ake samu wajen samun zaman lafiya a tsakanin al’umma da ke bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp