Home General Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya...

Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya cikin watanni 6

Babban Hafsan Hafsoshin Sojoin Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa ƴan ta’addan Boko Haram 129,417 da iyalansu sun mika wuya ga jami’an tsaro tsakanin ranar 10 ga watan Yuli zuwa 9 ga watan Disamban wannan shekara ta 2024.

Babbabn hafsan rundunar sojin ƙasa na Najeriya ya bayyana haka ne a taron tsaro na Afrika karo na 18 da ke gudana a birnin Doha na ƙasar Qatar.

Taron, mai taken: “Haɓaka tsaro don samar da Zaman Lafiya wanda Mista Patrick Agbambu na ƙungiyar Watch Africa Initiative ya shirya, ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro daga ƙasashen Najeriya da Guinea Bissau da Gambia da Afirka ta Kudu da Kenya da kuma Qatar.

Janar Musa a jawabinsa ya bayyana cewa alkaluman sun hada da mayaka 30,426, mata 36,774, da yara 62,265.

A cewarsa, wannan nasara ta nuna ci gaban da ake samu wajen samun zaman lafiya a tsakanin al’umma da ke bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp