Home General Gwamnonin Najeriya sun yi taro a kan dokar haraji

Gwamnonin Najeriya sun yi taro a kan dokar haraji

Ƙungiyar gwamnonin Najeriya ta yi wani taro a cikin dare a hedikwatarta da ke birnin Abuja, inda rahotanni ke cewa sun tattauna abubuwa da dama ciki har da batun ƙudirin dokar haraji da ta janyo cece-ku-ce a ƙasar.

Babu dai bayani daga gwamnonin a kan abin da taron nasu ya cimma wa, amma rahotanni daga jaridun ƙasar sun ce batun ƙudirin dokar harajin ne jigo a zaman gwamnonin na jiya Laraba da daddare.

Gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki ne suka fi yawa a taron, inda aƙalla 15 suka halarta, sai gwamnoni biyu daga jam’iyyar Labour da kuma na APGA ɗaya.

Ƙudirin dokar harajin wanda shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar wa majalisar dokokin ƙasar ya janyo suka da ƙorafi daga masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnonin ƙasar a ƙarƙashin majalisar ƙoli ta tattalin arziki, da gwamnoni da ƴan majalisa daga yankin arewa da ma ƙungiyoyi da dama.

Gwamnonin Arewa 19 kuma sun bayyana rashin goyon bayan su ga wasu sassa na ƙudirin, tare da neman a gaggauta janye shi daga majalisar dokokin tarayya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp