Home General Gwamnonin Najeriya sun yi taro a kan dokar haraji

Gwamnonin Najeriya sun yi taro a kan dokar haraji

Ƙungiyar gwamnonin Najeriya ta yi wani taro a cikin dare a hedikwatarta da ke birnin Abuja, inda rahotanni ke cewa sun tattauna abubuwa da dama ciki har da batun ƙudirin dokar haraji da ta janyo cece-ku-ce a ƙasar.

Babu dai bayani daga gwamnonin a kan abin da taron nasu ya cimma wa, amma rahotanni daga jaridun ƙasar sun ce batun ƙudirin dokar harajin ne jigo a zaman gwamnonin na jiya Laraba da daddare.

Gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki ne suka fi yawa a taron, inda aƙalla 15 suka halarta, sai gwamnoni biyu daga jam’iyyar Labour da kuma na APGA ɗaya.

Ƙudirin dokar harajin wanda shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar wa majalisar dokokin ƙasar ya janyo suka da ƙorafi daga masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnonin ƙasar a ƙarƙashin majalisar ƙoli ta tattalin arziki, da gwamnoni da ƴan majalisa daga yankin arewa da ma ƙungiyoyi da dama.

Gwamnonin Arewa 19 kuma sun bayyana rashin goyon bayan su ga wasu sassa na ƙudirin, tare da neman a gaggauta janye shi daga majalisar dokokin tarayya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp