Home General Najeriya za ta nemi bashi don cike giɓin naira tiriliyan 13 a...

Najeriya za ta nemi bashi don cike giɓin naira tiriliyan 13 a kasafin kuɗin baɗi

Ministan kuɗi da tattalin arziƙi na Najeriya Wale Edun ya bayyana cewa gwamnatin ƙasar za ta nemi bashin naira tiriliyan 13 don cike giɓin da ke cikin kasafin kuɗin shekara mai zuwa.

A jawabin da ya gabatar gaban manema labarai bayan halartar taron majalisar tattalin arziƙi da ya gudana a fadar shugaban ƙasa ta Villa da ke Abuja, Mr Edun ya ce bashin ne kaɗai hanyar da Najeriya za ta iya magance matsalar ta giɓin kasafin kuɗi a wannan karon.

Jumular kuɗin gudanar da ayyuka da ke cikin kasafin ya kai naira tiriliyan 34 da biliyan 8 daga cikin ƙunshin kasafin na naira tiriliyan 47 da biliyan 9 wanda ke nuna ƙaruwar kashi 36.8 daga kasafin 2024.

Jumullar giɓin da ke ƙunshe a kasafin na bana na matsayin naira tiriliyan 13 da biliyan guda wato kashi 3.39 na ma’aunin tattalin arziƙi na GDP.

A cewar Mr Edun an gudanar da kasafin kuɗin na baɗi ne bisa ga duba ga irin gagarumin ci gaban da ƙasar ta samu ƙarkashin jagorancin watanni 18 da shugaba Tinubu ya shafe a kan kujerar mulkin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp