Home General Najeriya za ta nemi bashi don cike giɓin naira tiriliyan 13 a...

Najeriya za ta nemi bashi don cike giɓin naira tiriliyan 13 a kasafin kuɗin baɗi

Ministan kuɗi da tattalin arziƙi na Najeriya Wale Edun ya bayyana cewa gwamnatin ƙasar za ta nemi bashin naira tiriliyan 13 don cike giɓin da ke cikin kasafin kuɗin shekara mai zuwa.

A jawabin da ya gabatar gaban manema labarai bayan halartar taron majalisar tattalin arziƙi da ya gudana a fadar shugaban ƙasa ta Villa da ke Abuja, Mr Edun ya ce bashin ne kaɗai hanyar da Najeriya za ta iya magance matsalar ta giɓin kasafin kuɗi a wannan karon.

Jumular kuɗin gudanar da ayyuka da ke cikin kasafin ya kai naira tiriliyan 34 da biliyan 8 daga cikin ƙunshin kasafin na naira tiriliyan 47 da biliyan 9 wanda ke nuna ƙaruwar kashi 36.8 daga kasafin 2024.

Jumullar giɓin da ke ƙunshe a kasafin na bana na matsayin naira tiriliyan 13 da biliyan guda wato kashi 3.39 na ma’aunin tattalin arziƙi na GDP.

A cewar Mr Edun an gudanar da kasafin kuɗin na baɗi ne bisa ga duba ga irin gagarumin ci gaban da ƙasar ta samu ƙarkashin jagorancin watanni 18 da shugaba Tinubu ya shafe a kan kujerar mulkin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp