Home General Ƴan bindiga sun sake sace mutane 46 a jihar Zamfara ta Najeriya

Ƴan bindiga sun sake sace mutane 46 a jihar Zamfara ta Najeriya

Ƴan bindiga a jihar Zamfara ta Najeriya, sun yi garkuwa da aƙalla mutane 46 yayin wani hari da suka kai kan al’ummar garin Gana da ke jihar ta yankin arewa maso yammacin ƙasar, lamarin da ke zayyana bayyana yadda matsalolin tsaro ke ci gaba da ta’azzara a yankin duk da namijin ƙoƙarin da mahukuntan ƙasar ke iƙirarin yi don baiwa al’umma kariya.

Bayanan masu tayar da hankali na zuwa a dai dai lokacin da wasu majiyoyi ke cewa ɗan bindigar daji Dogo Giɗe ya sanyawa wasu garuruwa 23 a ƙaramar hukumar tsafe duk cikin jihar ta Zamfara harajin naira miliyan 100 bisa sharaɗin kai musu hari matuƙar suka gaza haɗa adadin kuɗin da ya nema, ko da ya ke a zantawar da sashen Hausa na RFI ya yi da mazauna yankin sun ce babu batu mai kama da wannan barazana.

Kafofin yaɗa labarai na ciki da wajen Najeriya sun ruwaito yadda gomman ƴan bindigar suka farmaki garin Gana a jihar Zamfara cikin ranakun ƙarshen mako tare da buɗe wuta kan jama’a wanda ya kai ga ƙone tarin gidajen da wuraren sana’ar jama’a gabanin sace tarin mutane ciki har da mata da ƙananan yara.

Wannan hari na zuwa bayan makamancinsa a watan da ya gabata, wanda shi ma ya kai ga sace tarin mutane, a wani yanayi da ake ganin dawowar makamantan hare-haren da kuwa garkuwa da mutane.

A lokuta da dama jami’an tsaron Najeriya na ci gaba da nanata cewa sun kame tarin jiga-jigan masu garkuwa da mutane a wannan jiha, yayinda suke neman wasu ruwa a jallo.

Kusan dukkanin jihohin yankin na arewa maso yammacin Najeriya na fuskantar matsalolin ɓatagarin kama daga ƴan bindiga da kuma ƴan ta’addan waɗanda suka hana jama’a sakat tare da kassara harkokin noma da kasuwanci, lamarin da ya ta’azzara talauci da yunwar da al’umma ke fama da ita.

Ko a makon da ya gabata, sai da ƴan bindigar, suka tare wata motocin safa tare da banka mata wuta bayan sace ilahirin fasinjan da ke cikinta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp