Home General Chadi ta daƙile harin da ƴan ta’adda suka kai fadar shugaban ƙasa

Chadi ta daƙile harin da ƴan ta’adda suka kai fadar shugaban ƙasa

Chadi ta sanar da daƙile wani hari da ta ce mayaƙa ɗauke da muggan makamai sun kai fadar shugaban ƙasar da ke birnin N’Djamena a yammacin ranar Laraba inda mutane 19 suka mutu.

Kakakin gwamnatin Chadi Abderaman Koulamallah ya ce maharan 24 ne suka farwa fadar kuma dakarun Sojin ƙasar sun hallaka 18 daga cikinsu, ko da ya ke suma sun kashe jami’i guda.

Koulamallah ya ce baya ga mutanen 19 da suka mutu yayin musayar wuta tsakanin Sojin ƙasar da maharan akwai kuma wasu mutum 6 daga ɓangaren maharan da kuma 3 daga ɓangaren jami’an tsaron Chadi ciki har da wani da ke cikin mawuyacin hali.

Sa’o’i ƙalilan bayan harin ne Koulamallah ya fito a wani bidiyo da aka yaɗa kai tsaye ga al’ummar ƙasar, inda ya ke zagaye da Sojoji ɗaure da bindiga a ɗamararsa ya na sanar da daƙile yunƙurin kai harin fadar shugaban ƙasa.

Harin na zuwa a dai dai lokacin da ministan harkokin wajen China Wang Yi ke ziyarar aiki a Chadin, kuma jim kaɗan bayan ganawarsa da shugaba Mahamat Idris Deby wanda ke cikin fadar lokacin faruwar harin.

A shekarar 2021 ne Mahamat Deby ya ƙarbi ragamar ƙasara matsayin shugaban riƙon ƙwarya bayan mutuwar mahaifinsa a fagen dafa yayin karan batta da ƴan tawaye, jagoran da ya fara mulkar Chadi tun bayan juyin mulkin da ya yi a shekarun 1990.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa Boko Haram ce ta ƙaddamar da harin kan fadar shugaban ƙasar na Chadi sai dai Koulamallah ya ce maharan ba Boko Haram ba ne haka zalika ba ƴan tawaye ba ne, face wasu wawayen mashaya.

A gefe guda wata majiya ta shaidawa Reuters cewa, harin ka iya zama na ta’addanci.

Wasu ganau sun ce tun farko motoci 3 ne suka tsaya a ginin gab da fadar shugaban ƙasar kuma nan ta ke suka fara harbe-harbe sai dai cikin gaggawa Sojoji suka daƙile barazanar tasu.

Mazauna yankunan sun ce sun jiyo ƙarar harbe-harbe na tsawon lokaci gabanin lafawarsu a gab da fadar shugaban na Chadi.

Harin dai ya zo ƙasa da makwanni 2 bayan Chadi ta gudanar da babban zaɓenta haka zalika kwanaki ƙalilan bayan ficewar Sojin Faransa daga ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp