Home General Chadi ta daƙile harin da ƴan ta’adda suka kai fadar shugaban ƙasa

Chadi ta daƙile harin da ƴan ta’adda suka kai fadar shugaban ƙasa

Chadi ta sanar da daƙile wani hari da ta ce mayaƙa ɗauke da muggan makamai sun kai fadar shugaban ƙasar da ke birnin N’Djamena a yammacin ranar Laraba inda mutane 19 suka mutu.

Kakakin gwamnatin Chadi Abderaman Koulamallah ya ce maharan 24 ne suka farwa fadar kuma dakarun Sojin ƙasar sun hallaka 18 daga cikinsu, ko da ya ke suma sun kashe jami’i guda.

Koulamallah ya ce baya ga mutanen 19 da suka mutu yayin musayar wuta tsakanin Sojin ƙasar da maharan akwai kuma wasu mutum 6 daga ɓangaren maharan da kuma 3 daga ɓangaren jami’an tsaron Chadi ciki har da wani da ke cikin mawuyacin hali.

Sa’o’i ƙalilan bayan harin ne Koulamallah ya fito a wani bidiyo da aka yaɗa kai tsaye ga al’ummar ƙasar, inda ya ke zagaye da Sojoji ɗaure da bindiga a ɗamararsa ya na sanar da daƙile yunƙurin kai harin fadar shugaban ƙasa.

Harin na zuwa a dai dai lokacin da ministan harkokin wajen China Wang Yi ke ziyarar aiki a Chadin, kuma jim kaɗan bayan ganawarsa da shugaba Mahamat Idris Deby wanda ke cikin fadar lokacin faruwar harin.

A shekarar 2021 ne Mahamat Deby ya ƙarbi ragamar ƙasara matsayin shugaban riƙon ƙwarya bayan mutuwar mahaifinsa a fagen dafa yayin karan batta da ƴan tawaye, jagoran da ya fara mulkar Chadi tun bayan juyin mulkin da ya yi a shekarun 1990.

Wasu majiyoyi sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa Boko Haram ce ta ƙaddamar da harin kan fadar shugaban ƙasar na Chadi sai dai Koulamallah ya ce maharan ba Boko Haram ba ne haka zalika ba ƴan tawaye ba ne, face wasu wawayen mashaya.

A gefe guda wata majiya ta shaidawa Reuters cewa, harin ka iya zama na ta’addanci.

Wasu ganau sun ce tun farko motoci 3 ne suka tsaya a ginin gab da fadar shugaban ƙasar kuma nan ta ke suka fara harbe-harbe sai dai cikin gaggawa Sojoji suka daƙile barazanar tasu.

Mazauna yankunan sun ce sun jiyo ƙarar harbe-harbe na tsawon lokaci gabanin lafawarsu a gab da fadar shugaban na Chadi.

Harin dai ya zo ƙasa da makwanni 2 bayan Chadi ta gudanar da babban zaɓenta haka zalika kwanaki ƙalilan bayan ficewar Sojin Faransa daga ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp