Home General NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

Hukumar hana sha da Fataucin miyagun Kwayoyi (NDLEA) ta kasa reshen jihar Kano, ta sami nasarar kama wasu Matasa 18 wadanda ta ke zargin suna da alaka da kayan maye.

Kakakin hukumar na jihar Sadik Muhammad Maigatari ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba manema labarai a ranar Jumu’a, inda ya ce nasarar ta samu ne ka karkashin “Operation Hana Maye”, wanda suke kokarin kakkabe dukkan wasu harkokin kayan maye ko kuma ta’ammali dasu a lungu da sako na jihar Kano.

A cewar hukumar, “Mun sami nasarar ne a wuraren da Matasan ke taruwa a unguwannin Fagge, Kwarin Kaya, Kofar Wambai, da kuma Kofar Mata, harma muka sami nasarar kama Tabar Wiwi, Sholisho da kuma makamai hadin gida masu haɗarin gaske”.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, a yayin sumamen wasu gungun Matasa ɗauke da makamai sun fito suna yi wa jami’an hukumar barazana, amma sun sami nasarar kama biyu daga cikin su inda suke tsaka da neman ragowar domin su fuskanci hukunci.

A karshe hukumar ta bada tabbacin ci-gaba da fatattakar dukkan masu yin wata mu’amala da kayan maye a fadin jihar, ta yadda rayuwar al’umma zata inganta yadda ya kamata.

Gwagwarmayar Nemawa ‘Yan Najeriya Sauki Zakuyi Ba Iya Ma’aikata Ba – Sakon Gama Ga NLC

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp