Home General NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

Hukumar hana sha da Fataucin miyagun Kwayoyi (NDLEA) ta kasa reshen jihar Kano, ta sami nasarar kama wasu Matasa 18 wadanda ta ke zargin suna da alaka da kayan maye.

Kakakin hukumar na jihar Sadik Muhammad Maigatari ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba manema labarai a ranar Jumu’a, inda ya ce nasarar ta samu ne ka karkashin “Operation Hana Maye”, wanda suke kokarin kakkabe dukkan wasu harkokin kayan maye ko kuma ta’ammali dasu a lungu da sako na jihar Kano.

A cewar hukumar, “Mun sami nasarar ne a wuraren da Matasan ke taruwa a unguwannin Fagge, Kwarin Kaya, Kofar Wambai, da kuma Kofar Mata, harma muka sami nasarar kama Tabar Wiwi, Sholisho da kuma makamai hadin gida masu haɗarin gaske”.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, a yayin sumamen wasu gungun Matasa ɗauke da makamai sun fito suna yi wa jami’an hukumar barazana, amma sun sami nasarar kama biyu daga cikin su inda suke tsaka da neman ragowar domin su fuskanci hukunci.

A karshe hukumar ta bada tabbacin ci-gaba da fatattakar dukkan masu yin wata mu’amala da kayan maye a fadin jihar, ta yadda rayuwar al’umma zata inganta yadda ya kamata.

Gwagwarmayar Nemawa ‘Yan Najeriya Sauki Zakuyi Ba Iya Ma’aikata Ba – Sakon Gama Ga NLC

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp