Home General NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

Hukumar hana sha da Fataucin miyagun Kwayoyi (NDLEA) ta kasa reshen jihar Kano, ta sami nasarar kama wasu Matasa 18 wadanda ta ke zargin suna da alaka da kayan maye.

Kakakin hukumar na jihar Sadik Muhammad Maigatari ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba manema labarai a ranar Jumu’a, inda ya ce nasarar ta samu ne ka karkashin “Operation Hana Maye”, wanda suke kokarin kakkabe dukkan wasu harkokin kayan maye ko kuma ta’ammali dasu a lungu da sako na jihar Kano.

A cewar hukumar, “Mun sami nasarar ne a wuraren da Matasan ke taruwa a unguwannin Fagge, Kwarin Kaya, Kofar Wambai, da kuma Kofar Mata, harma muka sami nasarar kama Tabar Wiwi, Sholisho da kuma makamai hadin gida masu haɗarin gaske”.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, a yayin sumamen wasu gungun Matasa ɗauke da makamai sun fito suna yi wa jami’an hukumar barazana, amma sun sami nasarar kama biyu daga cikin su inda suke tsaka da neman ragowar domin su fuskanci hukunci.

A karshe hukumar ta bada tabbacin ci-gaba da fatattakar dukkan masu yin wata mu’amala da kayan maye a fadin jihar, ta yadda rayuwar al’umma zata inganta yadda ya kamata.

Gwagwarmayar Nemawa ‘Yan Najeriya Sauki Zakuyi Ba Iya Ma’aikata Ba – Sakon Gama Ga NLC

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp