Home General NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

NDLEA ta kama matsala masu shaye -shaye 18 a Kano

Hukumar hana sha da Fataucin miyagun Kwayoyi (NDLEA) ta kasa reshen jihar Kano, ta sami nasarar kama wasu Matasa 18 wadanda ta ke zargin suna da alaka da kayan maye.

Kakakin hukumar na jihar Sadik Muhammad Maigatari ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya raba manema labarai a ranar Jumu’a, inda ya ce nasarar ta samu ne ka karkashin “Operation Hana Maye”, wanda suke kokarin kakkabe dukkan wasu harkokin kayan maye ko kuma ta’ammali dasu a lungu da sako na jihar Kano.

A cewar hukumar, “Mun sami nasarar ne a wuraren da Matasan ke taruwa a unguwannin Fagge, Kwarin Kaya, Kofar Wambai, da kuma Kofar Mata, harma muka sami nasarar kama Tabar Wiwi, Sholisho da kuma makamai hadin gida masu haɗarin gaske”.

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, a yayin sumamen wasu gungun Matasa ɗauke da makamai sun fito suna yi wa jami’an hukumar barazana, amma sun sami nasarar kama biyu daga cikin su inda suke tsaka da neman ragowar domin su fuskanci hukunci.

A karshe hukumar ta bada tabbacin ci-gaba da fatattakar dukkan masu yin wata mu’amala da kayan maye a fadin jihar, ta yadda rayuwar al’umma zata inganta yadda ya kamata.

Gwagwarmayar Nemawa ‘Yan Najeriya Sauki Zakuyi Ba Iya Ma’aikata Ba – Sakon Gama Ga NLC

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp