Home General Majalisar Dattawan Najeriya za ta binciki zarge-zargen Tchiani kan Najeriya

Majalisar Dattawan Najeriya za ta binciki zarge-zargen Tchiani kan Najeriya

Majalisar dattawan Najeriya ta ba da umurnin binciken zarge zargen da shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani ya yi na cewa gwamnatin Najeriya na haɗa kai da Faransa wajen kawo cikas ga tsaron ƙasarsa.

Umarnin na zuwa ne bayan wani ƙuduri da shugaban kwamitin tsaro na majaliar, Sanata Shehu Buba ya gabatar, inda ya jaddada cewa babban abin damuwa shi ne yadda Tchiani ya zargi mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, da tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta ƙasa, Ahmed Rufai, da hannu dumu-dumu wajen yi wa ƙasarsa bita-da-ƙulli.

Cikin zarge-zagen nasa, Tchiani ya ce gwamnatin Najeriya na taimaka wa ƙungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa da ke arewa maso yammacin ƙasar, wajen kafa sansanoni a Sokoto da Zamfara da kuma Kebbi, sannan suna amfani da wasu sansanonin sojoji a Najeriya domin kai hari kan bututun man Nijar da kuma kawo barazanar tsaro a ƙasarsa.

A martaninsa a zaman majalisar, mataimakin shugaban majalisar, sanata Barau Jibrin wanda ya jagoranci zaman ya amince da matsayar da ta buƙaci kwamiti kan tsaron ƙasar da kwaminitin harkokin ƙasashen waje su gudanar da bincike su kuma gabatar da rahoton nan da makonni huɗu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp