Home General Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin...

Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin zakara

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bawa Jami’ar Bayero umarnin dakatar da rushe -rushen da ta ke yi a garin Rimin Zakara.

Gwamnan ya bada umarnin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziya da kuma jajen abinda ya faru ga alummar yankin.

Abba Kabir ya kuma yiwa alummar alkawarin kawo karshen rikicin filayen da ke gudana tsakanin Jami’ar BUK da alummar Rimin Zakara wanda ya shafe sama da shekaru 30.

Dangane da wadanda suka rasa rayukansu gwamna Abba kabir ya bayar da umarnin kafa wani kwamiti da zai binciki lamarin tare da daukar dawainiyar iyalansu.

Hakazalika Gwamnan ya ba da umarni samawa alummar yankin asibitin sha -ka-tafi tare da Gina musu masallacin juma’a.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na bayar da umarnin daukar nauyin wadanda Suka Sami raunuka sakamakon abinda ya faru a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp