Home General Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin...

Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin zakara

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bawa Jami’ar Bayero umarnin dakatar da rushe -rushen da ta ke yi a garin Rimin Zakara.

Gwamnan ya bada umarnin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziya da kuma jajen abinda ya faru ga alummar yankin.

Abba Kabir ya kuma yiwa alummar alkawarin kawo karshen rikicin filayen da ke gudana tsakanin Jami’ar BUK da alummar Rimin Zakara wanda ya shafe sama da shekaru 30.

Dangane da wadanda suka rasa rayukansu gwamna Abba kabir ya bayar da umarnin kafa wani kwamiti da zai binciki lamarin tare da daukar dawainiyar iyalansu.

Hakazalika Gwamnan ya ba da umarni samawa alummar yankin asibitin sha -ka-tafi tare da Gina musu masallacin juma’a.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na bayar da umarnin daukar nauyin wadanda Suka Sami raunuka sakamakon abinda ya faru a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp