Home General Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin...

Gwamnan Kano ya bawa Jami’ar Bayero Umarnin dakatar da rushe-rushe a Rimin zakara

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bawa Jami’ar Bayero umarnin dakatar da rushe -rushen da ta ke yi a garin Rimin Zakara.

Gwamnan ya bada umarnin ne lokacin da ya kai ziyarar ta’aziya da kuma jajen abinda ya faru ga alummar yankin.

Abba Kabir ya kuma yiwa alummar alkawarin kawo karshen rikicin filayen da ke gudana tsakanin Jami’ar BUK da alummar Rimin Zakara wanda ya shafe sama da shekaru 30.

Dangane da wadanda suka rasa rayukansu gwamna Abba kabir ya bayar da umarnin kafa wani kwamiti da zai binciki lamarin tare da daukar dawainiyar iyalansu.

Hakazalika Gwamnan ya ba da umarni samawa alummar yankin asibitin sha -ka-tafi tare da Gina musu masallacin juma’a.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na bayar da umarnin daukar nauyin wadanda Suka Sami raunuka sakamakon abinda ya faru a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp