Home General Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Jami’ar Al-istiqama da ke garin Sumaila ta nada sabon Sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Sunusi a matsayin sabon chancilor.

Naɗin nasa wanda ya gudana a masarautar Dutse a yau Alhamis 6 ga watan Fabrairu 2024, na zuwa ne biyo bayan karewar wa’adin Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.

Da yake miƙa takardar naɗin mamallakin Jami’ar Sanatan Kano ta Kudu Sulaiman Abdulraman Kawu Sumaila, ya bayyana daɗaɗɗiyar alaƙarsu da masarautar Dutse, wanda hakan ya sanya hukumar gudanarwa jami’ar taga dacewar baiwa Mai martaba Sarkin Dutse dama domin zama Chancellor na Jami’ar, duba da yadda masautar ke baiwa addinin musulunci muhimmanci matuƙa dai dai da yadda aka ɗora manufar gudanar da Jami’ar.

Da yake jawabi mai martaba sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sunusi, ya nuna jin daɗinsa bisa karrama masarautar tare da godewa wanda ya assasa jami’ar da sauran hukumomin gudanarwarta.

Ya kuma ƙara da cewa tun abaya sun san za’azo wannan gaɓa duba da irin alaƙa ta mutunci da girmanawa dake tsakanin masarautar da yankin Sumaila.

Sarkin ya kuma yi alƙawarin bada gudunmawar masauatar ɗari bisa ɗari domin ci gaban wannan jami’a dama al’umma baki ɗaya.

Zuwa yanzu dai jami’ar ta samu sahalewar gudanarwa na din-din-din daga hukumar dake kula da jami’o’i ta ƙasa NUC bayan tsallake zangon gwaji da jami’ar tayi na tsawon shekaru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp