Home General Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Sarki Dutsen ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama

Jami’ar Al-istiqama da ke garin Sumaila ta nada sabon Sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Sunusi a matsayin sabon chancilor.

Naɗin nasa wanda ya gudana a masarautar Dutse a yau Alhamis 6 ga watan Fabrairu 2024, na zuwa ne biyo bayan karewar wa’adin Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero.

Da yake miƙa takardar naɗin mamallakin Jami’ar Sanatan Kano ta Kudu Sulaiman Abdulraman Kawu Sumaila, ya bayyana daɗaɗɗiyar alaƙarsu da masarautar Dutse, wanda hakan ya sanya hukumar gudanarwa jami’ar taga dacewar baiwa Mai martaba Sarkin Dutse dama domin zama Chancellor na Jami’ar, duba da yadda masautar ke baiwa addinin musulunci muhimmanci matuƙa dai dai da yadda aka ɗora manufar gudanar da Jami’ar.

Da yake jawabi mai martaba sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sunusi, ya nuna jin daɗinsa bisa karrama masarautar tare da godewa wanda ya assasa jami’ar da sauran hukumomin gudanarwarta.

Ya kuma ƙara da cewa tun abaya sun san za’azo wannan gaɓa duba da irin alaƙa ta mutunci da girmanawa dake tsakanin masarautar da yankin Sumaila.

Sarkin ya kuma yi alƙawarin bada gudunmawar masauatar ɗari bisa ɗari domin ci gaban wannan jami’a dama al’umma baki ɗaya.

Zuwa yanzu dai jami’ar ta samu sahalewar gudanarwa na din-din-din daga hukumar dake kula da jami’o’i ta ƙasa NUC bayan tsallake zangon gwaji da jami’ar tayi na tsawon shekaru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp