Home General An gudanar da Jana’idar Dan Zago

An gudanar da Jana’idar Dan Zago

An gudanar da jana’izar Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Dan Zago, tsohon shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano.

An gudanar da jana’izar a Kofar Kudu, dake fadar mai martaba Sarkin Kano Dr. Muhammadu Sanusi II.

Jana’izar ta samu halartar fitattun mutane da suka hadar da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II, da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Dan Zago, ya rasu yana da shekaru 74, sannan ya bar Mata 4 da yaya 37 sai kuma jikoki da dama.

Bayan kammala jana’izar Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya jagoranci zuwa gidan marigayin, domin yi musu ta’aziyyar rashin da suka yi.

Sauran wadanda suka je ta’aziyyar sun hadar da tsohon gwamnan Kano Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso da mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo da shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Jibrin Falgore sun shiga gidan marigayin inda suka yi addu’oi domin nema masa gafarar Allah.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp