Home General MTN ya nemi gafarar ƴan Najeriya kan ƙarin kuɗin kira da na...

MTN ya nemi gafarar ƴan Najeriya kan ƙarin kuɗin kira da na data

Kamfanin sadarwa na MTN a Najeriya ya bai wa masu amfani da layukansa haƙauri kan ƙarin kuɗin kira da na data da kamfanin ya yi a ƴan kwanakin nan.

A farkon makon nan ne aka wayi gari da ƙarin kusan kashi 200 cikin ɗari, lamarin da ƴan ƙasar da dama suka yi Allah wadai da shi.

To sai dai cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar a shafinsa na X, ya ce yana sane da yadda masu amfani da layukansa suka nuna damuwa bayan da suka wayi gari kwatsam da ƙarin kusan kashi 200 na kuɗin data.

Kamfanin ya ce zai iya bayar da dalilan da suka sa ya ɗauki matakin ƙarin, to sai dai ya ce in ma ya yi hakan ba zai gamsar ba.

”Saboda da haka mun karɓi laifinmu, mun yi kuskure, muna bayar da haƙuri kan hakan, a kuma yafe mana”, a cewar kamfanin.

Ƙarin dai ya tayar da ƙura a Najeriya, lamarin da ya sa ƙungiyar ƙwadago ta ƙasar, NLC ta buƙaci al’umma su ƙaurace wa amfani da layukan manyan kamfanonin wayar daga ƙarfe 11 na safe zuwa 2:00 na rana a kullum daga yau Alhamis, 13 ga watan Fabarairu har zuwa 28 ga watan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp