Home General Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta zargin ɓatan bindigu kusan dubu 4

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta zargin ɓatan bindigu kusan dubu 4

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ƙaryata rahoton da ke zargin cewar, akwai bindigu dubu 3 da dari 907 da suka ɓace daga rumbun aje makamanta, inda ta ce babu gaskiya a cikin zargin da aka yi mata.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a yau Alhamis, ya ce zargin ya samo asali ne daga rahoton da ofishin babban mai binciken ƙudi na ƙasar ya gudanar daga tsakanin shekarar 2019, amma sai dai ya ce bai fayyace haƙiƙanin makaman da suka ɓace ba.

Ga dukkan alamu rahoton ya samo asali ne daga binciken da aka yi a shekarar 2019, mai yiwuwa bayanan da aka tattara sun zo ne kafin fara wa’adin Sifeto Janar na yanzu. Rahoton ya nuna cewa makamai dubu 3 da ɗari 907 ne  ba a san inda suka shigeba, ba ɓacewa aka ce sun yi ba, kamar yadda ake yadawa.

Wannan ƙarin haske da rundunar tayi dai ya biyo bayan wani rahoto ofishin mai bincike ƙudi na ƙasar ya miƙa wa kwamitin kula da harkokin jama’a na majalisar dattawar ƙasar, wanda ya yi ƙorafi game da saɓanin alƙaluman yawan makaman rundunar da aka samu.

A lokacin sauraron ƙorafin, kwamitin majalisar dattawan Najeriya ya nuna damuwa kan yadda bindigogi dubu 178 da ɗari 459 ciki har da ƙirar AK-47 dubu 88 da 78, aka yi zargin sun ɓace daga ofisoshin ƴansanda a faɗin ƙasar.

To amma a sanarwar da rundunar ta fitar a yau, ta ce alkaluma ba su wakilci asalin bindigun da rundunar ke da su a rumbun aje makamanta ba, domin ta yiwuwa lokacin binciken wasu bindigogin an fita aiki da su.

Ya kuma ce wasu daga cikin bindigogin sun ɓace ne a yayin wasu hare-haren da aka kai wa ƴansanda a lokacin da suke gudanar da aiki.

Kwamitin na majalisar dattawan Najeriya ya ɗage zamansa kan ƙorafin har zuwa ranar Litinin 17 ga watan Fabrairu nan, don bai wa rundunar ƴansandan ƙasar damar gabatar da bayanan alkaluman da aka samu saɓani a kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp