Home General Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta zargin ɓatan bindigu kusan dubu 4

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta zargin ɓatan bindigu kusan dubu 4

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ƙaryata rahoton da ke zargin cewar, akwai bindigu dubu 3 da dari 907 da suka ɓace daga rumbun aje makamanta, inda ta ce babu gaskiya a cikin zargin da aka yi mata.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a yau Alhamis, ya ce zargin ya samo asali ne daga rahoton da ofishin babban mai binciken ƙudi na ƙasar ya gudanar daga tsakanin shekarar 2019, amma sai dai ya ce bai fayyace haƙiƙanin makaman da suka ɓace ba.

Ga dukkan alamu rahoton ya samo asali ne daga binciken da aka yi a shekarar 2019, mai yiwuwa bayanan da aka tattara sun zo ne kafin fara wa’adin Sifeto Janar na yanzu. Rahoton ya nuna cewa makamai dubu 3 da ɗari 907 ne  ba a san inda suka shigeba, ba ɓacewa aka ce sun yi ba, kamar yadda ake yadawa.

Wannan ƙarin haske da rundunar tayi dai ya biyo bayan wani rahoto ofishin mai bincike ƙudi na ƙasar ya miƙa wa kwamitin kula da harkokin jama’a na majalisar dattawar ƙasar, wanda ya yi ƙorafi game da saɓanin alƙaluman yawan makaman rundunar da aka samu.

A lokacin sauraron ƙorafin, kwamitin majalisar dattawan Najeriya ya nuna damuwa kan yadda bindigogi dubu 178 da ɗari 459 ciki har da ƙirar AK-47 dubu 88 da 78, aka yi zargin sun ɓace daga ofisoshin ƴansanda a faɗin ƙasar.

To amma a sanarwar da rundunar ta fitar a yau, ta ce alkaluma ba su wakilci asalin bindigun da rundunar ke da su a rumbun aje makamanta ba, domin ta yiwuwa lokacin binciken wasu bindigogin an fita aiki da su.

Ya kuma ce wasu daga cikin bindigogin sun ɓace ne a yayin wasu hare-haren da aka kai wa ƴansanda a lokacin da suke gudanar da aiki.

Kwamitin na majalisar dattawan Najeriya ya ɗage zamansa kan ƙorafin har zuwa ranar Litinin 17 ga watan Fabrairu nan, don bai wa rundunar ƴansandan ƙasar damar gabatar da bayanan alkaluman da aka samu saɓani a kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp