Home General Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa...

Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa ƙasar

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da iƙirarin da jami’in kamfanin Binance, Tigran Gambaryan, wanda ya shafe wata takwas yana tsare a ƙasar, kan zarge-zargen rashawa.

A kwanakin baya ne aka gurfanar da Gambaryan- ɗan Amurka – a kotun Najeriya bisa zargin laifukan kuɗi.

To sai dai hukumomin Najeriya sun sake shi ne bayan shiga tsakani da gwamnatin Amurka ta yi.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Gambaryan ya yi ikirarin cewa kama shi da gwamnatin Najeriya ta yi ba bisa ƙa’ida ba ya sa tsohon shugaban ƙasar Amurka, Joe Biden ya kauce wa ganawar da ya shirya yi da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a yayin taron Majalisar Dinkin Duniya na 2024 (UNGA).

Ya kuma zargi mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kan lamarin, sannan ya ce gwamnatin Amurka ta rage yawan wakilan Najeriya da suka halarci taron na MDD.

Jami’in na Binance ya kuma zargi wasu ƴan majalisar ƙasar uku da neman cin hancin dala miliyan 150 daga wajensa.

To sai dai a martanin da gwamnatin ƙasar ta mayar masa, ta ce zarge-zargen nasa ba su da tushe balle makama.

Cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labaran ƙasar, Mohammed Idris ya fitar, ya bayyana iƙirarin Gambaryan a matsayin tsantsar ƙarya da gangan.

“Gwamnatin Najeriya ta damu matuƙa da zarge-zargen marasa tushe, da kuma kalaman ɓatanci da Tigran Gambaryan, da aka yi wa shari’a a Najeriya kwannan kan laifukan kuɗi,” a cewar sanarwar.

Ta kuma ƙara da cewa ”gwamnati ta ki amincewa da tayin da Binance ta yi na biyan dala miliyan biyar don sakin Mista Gambaryan, don yin sulhu da gwamnatin Amurka.”

A farkon shekarar da ta gabata ne dai gwamnatin Najeriya ta tsare Mista Gambaryan tare da abokin aikinsa, Nadeem Anjarwalla ɗan Kenya asalin Birtaniya mai shekara 37 bisa zargin laifukan ɓarnatar da kuɗi da hukumar EFCC ke bincike.

To amma a watan Maris ɗin shekarar Anjarwalla ya gudu daga wurin da ake tsare da su, ya kuma fice daga Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp