Home General Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa...

Gwamnatin Najeriya ta musanta zarge-zargen rashawa da jami’in Binance ya yi wa ƙasar

Gwamnatin tarayya ta yi watsi da iƙirarin da jami’in kamfanin Binance, Tigran Gambaryan, wanda ya shafe wata takwas yana tsare a ƙasar, kan zarge-zargen rashawa.

A kwanakin baya ne aka gurfanar da Gambaryan- ɗan Amurka – a kotun Najeriya bisa zargin laifukan kuɗi.

To sai dai hukumomin Najeriya sun sake shi ne bayan shiga tsakani da gwamnatin Amurka ta yi.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Gambaryan ya yi ikirarin cewa kama shi da gwamnatin Najeriya ta yi ba bisa ƙa’ida ba ya sa tsohon shugaban ƙasar Amurka, Joe Biden ya kauce wa ganawar da ya shirya yi da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a yayin taron Majalisar Dinkin Duniya na 2024 (UNGA).

Ya kuma zargi mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kan lamarin, sannan ya ce gwamnatin Amurka ta rage yawan wakilan Najeriya da suka halarci taron na MDD.

Jami’in na Binance ya kuma zargi wasu ƴan majalisar ƙasar uku da neman cin hancin dala miliyan 150 daga wajensa.

To sai dai a martanin da gwamnatin ƙasar ta mayar masa, ta ce zarge-zargen nasa ba su da tushe balle makama.

Cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labaran ƙasar, Mohammed Idris ya fitar, ya bayyana iƙirarin Gambaryan a matsayin tsantsar ƙarya da gangan.

“Gwamnatin Najeriya ta damu matuƙa da zarge-zargen marasa tushe, da kuma kalaman ɓatanci da Tigran Gambaryan, da aka yi wa shari’a a Najeriya kwannan kan laifukan kuɗi,” a cewar sanarwar.

Ta kuma ƙara da cewa ”gwamnati ta ki amincewa da tayin da Binance ta yi na biyan dala miliyan biyar don sakin Mista Gambaryan, don yin sulhu da gwamnatin Amurka.”

A farkon shekarar da ta gabata ne dai gwamnatin Najeriya ta tsare Mista Gambaryan tare da abokin aikinsa, Nadeem Anjarwalla ɗan Kenya asalin Birtaniya mai shekara 37 bisa zargin laifukan ɓarnatar da kuɗi da hukumar EFCC ke bincike.

To amma a watan Maris ɗin shekarar Anjarwalla ya gudu daga wurin da ake tsare da su, ya kuma fice daga Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp