Home General NNPCL ya musanta zargin rashin aukin man fetur ɗin da yake sayarwa

NNPCL ya musanta zargin rashin aukin man fetur ɗin da yake sayarwa

Babban kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya yi watsi da iƙirarin da wani mutum ya yi cewa man da kamfanin ke sayarwa bai kai na Dangote auki ba.

Cikin wani bidiyo da ya karaɗa shafukan sada zumunta an ga wani mutum da ya ce ya sayi man fetru daga kamfanin NNPCL a kan farashin naira 945, sannan ya sayi wani man a wani gidan mai da ke sauke man Dangote, a kan naira 925.

A cikin bidiyon mutumin ya yi iƙirarin cewa man Dangote ya zarta na kamfanin NNPLC daɗewa ana amfani da shi, inda har ya yi iƙirarin gwada mayukan biyu a injuna biyu, daga ƙarshe ya ce na NNPCL ya riga na Dangote ƙarewa da minituna fiye da 10.

To sai dai cikin wata sanarwar martani da NNPCL ɗin ya fitar ya ce gwajin da mutumin ya yi bai yi shi da ƙwarewa ba, sannan babu wata hujja ta kamawa a cikinsa.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa mafi yawan man da wannan gidan mai na NNPCL – da mutumin ya yi iƙirarin sayo man – daga kamfanin Dangote yake sayensa.

“NNPCL na jaddada ƙudirinsa na cewa man da yake sayarwa ana haɗa shi da ɗaya daga cikin manyan sidanarai masu inganci da ke taimakawa wajen tabbatar aukinsa da kuma rashin illa ga muhalli”, in ji sanarwar.

Daga ƙarshe ya gargaɗi masu irin wannan ɗabi’a cewa ba zai jure irin waɗannan ƙarairayi da ake shiryawa domin ɓata masa suna da kuma cutar da ƴan Najeriya ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp