Home General Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Tinubu ya yaba wa El-Rufai saboda ‘gina dimokraɗiyya’ a Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba wa tsohon gamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai kan gudunmowar da ya bayar a fannin dimoƙraɗiyyar ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, domin taya El-Rufai munar cika shekara 65 a duniya, Tinubu ya bayyana tsohon gwamnan na Kaduna da jagora, manazarci kuma ɗan siyasa.

”Irin gudunmowar da ya bayar wajen hidimta wa ƙasa da zama abin koyi ga ƴan baya, babban abin yabawa ne”, a cewar sanarwar.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa rawar da El-Rufai ya taka wajen kafuwar jam’iyyar APC, da kuma irin gudunmowar da ya bayar wajen nasarorin jam’iyyar a zaɓukan ƙasar uku da suka gabata, 2015 da 2019 da kuam 2023.

A shekarar 2015 ne aka zaɓi Mallam Nasir El-Rufai a matsayin gwamnan jihar Kaduna, inda ya yi wa’adin mulki biyu.

Bayan rantsar da Shugaba Tinubu a 2023 ya sanya sunan El-Rufai cikin jerin mutanen da yake son bai wa muƙaman ministoci, sai dai tsohon gwamnan bai tallake tantancewar majalisar dattawan ƙasar ba, lamarin da ya sa bai samu muƙamin ba.

Daga nan ne kuma dangantaka ta fara tsami tsakaninsa da Tinubu, inda a baya-bayan ya riƙa fitowa fili yana sukar manufofin gwamnatin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp