Home General Jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kashe mutum shida bisa ‘kuskure’ a Katsina

Jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kashe mutum shida bisa ‘kuskure’ a Katsina

Rahotanni daga jihar Katsina na cewa jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kashe mutum shida bisa ‘kuskure’ a lokacin da sojojin ke bin wani gungun masu garkuwa da mutane.

Mazauna ƙauyen Zakka a Katsina sun ce jirgin sojin sun jefa bama-bamai a kan rukunun bukkoki, abin da ya janyo sanadiyyar kisan mutum shida.

Luguden wutar kamar yadda wani rahoto ya ce na zuwa ne bayan da wasu ƴanbindiga suka kai wa wani sansanin ƴansanda hari inda suka kashe jami’an guda biyu da ɗan sinitiri guda ɗaya.

Sai dai ƙungiyar Amnestiy International ta nemi da a gudanar da bincike.

Har kawo yanzu sojojin Najeriya ba su ce uffan ba dangane da harin na ‘kuskure’.

A baya dai sun sha bayyana cewa hare-hare irin waɗannan na kuskure ne kuma za a ɗauki matakan kawo ƙarshen afkuwar hakan a gaba.

Wannan ne dai karo na 10 da ake samun irin waɗannan hare-hare na kuskure a shekaru biyu sannan na 11 a tsawon shekaru takwas.

Ko a watan Janairun 2025 ma sai da aka samu irin wannan harin na kuskure a a jihar Zamfara inda fafaren hula 16 suka mutu.

A watan Disamban 2024 ma an samu irin wannan hari a jihar Sokoto wanda ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula 10.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp