Home General Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk...

Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk da dakatar da USAID

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin ci gaba da rike ma’aikatan lafiya 28,000 da Hukumar Raya Kasashe ta Amurka USAID ke daukar nauyinsu a baya, wanda shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da ayyukanta.

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Najeriya, Muhammad Pate, ya bayyana hakan, yayin hira da wata kafar talabijin ta ƙasar, inda ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin shigar da ma’aikatan cikin tsarin kiwon lafiyar ƙasar tare da rage dogaro da tallafi da ƙasashen ƙetare ke bayarwa.

Mista Pate ya bayyana gagarumar gudunmawar da gwamnatin Amurka ke bayarwa a fannin kiwon lafiyar Najeriya, musamman a bangaren cutar kanjamau, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, sai dai ya jaddada cewa Najeriya ta kuduri aniyar daukar nauyin sashen kula da lafiyarta da kuma rage dogaro da tallafin da take samu daga waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp