Home General Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk...

Najeriya za ta ci gaba da rike ma’aikatan lafiya dubu 28 duk da dakatar da USAID

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin ci gaba da rike ma’aikatan lafiya 28,000 da Hukumar Raya Kasashe ta Amurka USAID ke daukar nauyinsu a baya, wanda shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da ayyukanta.

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Najeriya, Muhammad Pate, ya bayyana hakan, yayin hira da wata kafar talabijin ta ƙasar, inda ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin shigar da ma’aikatan cikin tsarin kiwon lafiyar ƙasar tare da rage dogaro da tallafi da ƙasashen ƙetare ke bayarwa.

Mista Pate ya bayyana gagarumar gudunmawar da gwamnatin Amurka ke bayarwa a fannin kiwon lafiyar Najeriya, musamman a bangaren cutar kanjamau, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, sai dai ya jaddada cewa Najeriya ta kuduri aniyar daukar nauyin sashen kula da lafiyarta da kuma rage dogaro da tallafin da take samu daga waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp